16/03/2026
Firaministan Isra’ila ya musanta jita-jitar mutuwarsa
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya fitar da wani bidiyo a shafinsa na sada zumunta inda ya musanta jita-jitar da ke cewa ya mutu sakamakon harin da Iran ta kai kan birnin Tel Aviv.
A cikin bidiyon, Netanyahu ya bayyana cewa yana cikin koshin lafiya, yana mai kira ga jama’a da su yi watsi da rahotannin da ba su da tushe da ke yawo a kafafen sada zumunta.
Jita-jitar mutuwar tasa ta bazu ne bayan wasu rahotanni da ke cewa Iran ta kai hare-hare kan wasu wurare a Isra’ila, lamarin da ya haddasa cece-kuce a dandalin intanet. Sai dai hukumomin Isra’ila sun tabbatar da cewa labaran mutuwar firaministan ba gaskiya ba ne.
Rahotanni sun kuma nuna cewa rundunar Iran Revolutionary Guard Corps (IRGC) ta sha alwashin kai hari kan Netanyahu kafin kawo karshen rikicin da ke tsakanin Iran da Isra’ila.