29/01/2026
“Ganduje fa neman shi ake yi, a Kotuna wurin guda biyu, an ce masa ya zo yaƙi zuwa, amma sai ga shi a gidan Gwamnati ga ‘yan sanda ga jami'an tsaro ga komai, k**ar wasan kwaikwayo? - Barr. Abba Hikima.
Barista Abba Hikima ya bayyana haka ne a cikin wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Manhajar Facebook, inda ya bayyana cewa yanzu haka Kotuna biyu suna neman Ganduje bisa tuhumar da ake masa na Handama, ya ce maimakon a k**a shi a lokacin da ya zo gidan Gwamnatin Kano, sai ba a yi haka ba, duk da akwai jami'an tsaro a wurin.