14/11/2025
KADAN DAGA CIKIN ABUBUWAN DA SUKE HANA MACE SHIGA ALJANNAH KODA KUWA TANA SALLAH:-
1) Duk Matar da take da aure tayi zina.
2)Duk Matar da ta Mallaki Mijinta ta hanyar asiri ko ta hanyar tsafi
3)Duk Matar data Hana kishiyarta ta zauna da Mijinta lafiya
4)Duk matar da ta raba mijinta da 'ya'yansa,ko ta Hanyar Asiri ko Yaudara
5)Duk matar data raba mijinta da Yan uwansa ta hanyar asiri ko yaudara
6)Duk matar da tayi asiri akan saukarwa kishiyarta jinin haila duk ranar kwananta sai haila tazo mata
7)Duk matar da tasa aka daure mahaifar kishiyarta,don kar ta haihu
8)Duk matar data dauko ciki a waje ta bawa mijinta,kuma ta tabbata ba nasa bane
9)Duk matar da tayi daurin baka ga mijinta don yayi mata kishiya Ma'anar baka shine: Duk ranar da zai kwana a dakin kishiyarta sai ya zamanto bana miji ba. Amma idan ya dawo dakin matsafiyar sai ya dawo namiji
10)Duk matar data nemi mijinta ya saketa,alhali baya cutar da ita.Kuma ba yadda ya iya
11)Duk matar da bata godewa mijinta bisa ga irin abubuwan da yake mata na Alkhairi
12)Duk matar da take cutar da mijinta da bakinta
13)Duk matar da batayin wankan janaba, bayan ta sadu da mijinta,ko batayin wankan haila ko biki
14)Duk matar da take tona asirin mijinta a cikin kawayenta
15)Duk matar da take annamimanci
16)Duk matar da take sa kayan da yake nuna tsiraicinta,irin wanda musulunci yake fada akan irin shigar yahudawa da nasara
17)Duk matar data kara gashi akan nata
18)Duk matar da tilastawa mijinta yayi mata wani abu wanda ba zai iya yi ba
19)Duk matar data dauki dan wani ta bashi Mama (Nono) bada izinin Mijinta ba
20)Duk matar da zata cewa Mijinta tunda muke dakai meka taba yi mini.
Dukkan wadannan Laifuka guda 20, ko wani guda daya a ciki, idan Mata ta mutu tanayi bazata shiga Aljannah ba, Koda zata shiga sai an Babbaka ta.