NURA ASHIRUGRAPHICSDesign

NURA ASHIRUGRAPHICSDesign Sunnah tudun wada graphics design

12/01/2025
Maigidanmu, Manzon Allah صلى الله عليه وسلمAnnabin gaskia ne, Annabin cika Alkawari ne 👇Zaka fahimci cewa wallahi Manzon...
30/10/2024

Maigidanmu, Manzon Allah صلى الله عليه وسلمAnnabin gaskia ne, Annabin cika Alkawari ne 👇

Zaka fahimci cewa wallahi Manzon Allah,صلى الله عليه وسلم Manzon Allah ne acikin Qissoshi da Hadisai Ingantattu, Shin Ko kasan alkawarin da Manzon Allah صلى الله عليه وسلمYayi wa Suraqa Bin Maliq tun yana raye Sai bayan mutuwar Manzon Allahصلى الله عليه وسلم alqawarinsa yacika??

Suraqa Bn Maliq yanadaga cikin sahabban Manzon Allahصلى الله عليه وسلم masu dogon tarihi, Wanda Yayi hidima wa musulunci , lokacin da Manzon Allah صلى الله عليه وسلمzaiyi hijira zuwa garin Madina don Addinin Allah Yasamu wajen Zama akan hanyarsa Shi da abokinsa Sayyidina Abubakar S**a hadu da Suraka Bn maliq anan suraqa yakarbi musulunci yace zaiyi aiki wa addini da Manzon Allah.صلى الله عليه وسلم
~ Yayin da Manzon Allah صلى الله عليه وسلمyajuya Zai tafi garin Madina suraqa Yace 'Ya Manzon Allah صلى الله عليه وسلمkamun Kyauta Wanda bazan taba mantawa da ita ba, Manzon Allah صلى الله عليه وسلمYace kasan "Kanbin zinare 👑" na Kan Sarkin farisa Sarki Qisra.

Suraqa Bn Maliq yace 'Eh ya Manzon Allah nasanshi , Manzon Allahصلى الله عليه وسلم Yace kaje nabaka Shi Kyauta , Yace Manzon yaushe Zan karbi wannan "Kanbin 👑" Annabi Yace bansani ba amma dai za'a baka Shi kaje, Suraqa Bn Maliq yace 'ya Manzon Allahصلى الله عليه وسلم Ko Zaka rubutamun arubuce don nasamu evidence Annabi Yace 'Eh a rubuta masa Sayyidina Abubakar yadauki paper 📜 da biro yarubuta masa Kyautar da Annabi yamasa.

Bayan Shekaru Manzon Allah,صلى الله عليه وسلمya rasu Sayyidina Abubakar Yarasu Sai Zamanin kalifancin Sayyidina Umar Bn Kathab Yatara mayaka da sojoji Yace aje ayaki Sarkin farisa Sarki Qisra, aka Yaki Sarki Qisra aka ci ganima akansa aka dauko wannan "Kanbin Zinare 👑 na sarkin farisa" , Suraqa Bn Maliq yaji labarin "Kanbin 👑 Sarki Qisra" an sameta cikin ganima Sai ya Hau doki Sai fadar Sayyidina Umar Bn Kathab tare da Wannan takardar 📜 Kyautan da Annabi ya masa.
~ Suraqa Bn Maliq Yana zuwa Sai yace wa Sayyidina Umar Bn nazo karban "Kanbina 👑" Yace Wani "Kanbi" Yace kanbin Sarki Qisra Umar Bn Kathab Yace Waya baka Yace Manzon Allah صلى الله عليه وسلم
Yace ina hujjarka daza tanuna cewa Annabi Yabaka wanann "Kanbin👑" yadauko takardar 📜 da Annabi ya rubuta masa ana budewa Sai akaga an rubuta :

" لقد أمر رسول الله صلى الله عليه وسلم لي سورقة بن ملك عن يلبس سواري و تاجه كسر"

"Hakika Manzon Allahصلى الله عليه وسلم Yayi umuri wa Suraqa Bn Maliq da ya sa Kanbin👑 Sarki Qisra".

Allahu Akbar nan take Sayyidina Umar Bn Kathab Yace wannan rubutun rubutun sayyidina Abubakar ne , don Umar yasan Abubakar bazaiyi Karya wa Manzon Allah صلى الله عليه وسلمnan aka Miki wa Suraqa bin Maliq Kanbin Sarki Qisra👑, Wanda Sai bayan rasuwar maigidanmu, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Allah yaci masa alkawarin da Manzon Allah صلى الله عليه وسلمYayi masa.

Wannan Shi Zai Kara maka yarda da Manzon Allah صلى الله عليه وسلمcewa Annabi manzone nagaske Kuma daga Allah , baya Magana bisa son rai da zucia (صلى الله عليه وسلم.🥰
By Nura Ashiru twd

MENENE AINAHIN TSORON ALLAH?*************************************Tsoron Allah ba wai yana nufin sanya dogayen kaya, Ko S...
28/10/2024

MENENE AINAHIN TSORON ALLAH?
*************************************
Tsoron Allah ba wai yana nufin sanya dogayen kaya, Ko Sanya rawani, Ko rike charbi, ko ajiye gemu, ko sanya dogon Hijabi bane. Ba kuma yana nufin yin siffah irin ta Malumta bane.

Tsoron Allah yana nufin BARIN SA'BON ALLAH saboda Jin tsoron gamuwarka dashi, Da kuma bin Allah sau da Qafa don kwadayin samun rahamarsa.

Tsoron Allah yana nufin ka rika jin kusancinsa gareka ako yaushe, aduk inda kake.

Daga cikin masu tsoron Allah daga magabata na kwarai, akwai wanda ya sanya hannu cikin bakinsa, ya Qakaro amai, ya amayar da dukkan abinda ke cikin cikinsa saboda wata lauma guda da ya hadiya wacce bai san asalinta ba.

Akwai wanda yayi tafiyar fiye da Mil Hamsin a Qafa domin mayar da wani alkalamin da ya karbi aronsa awajen abokinsa, ya taho dashi bisa mantuwa.

Akwai wata matar da ta rayu fiye da shekaru arba'in bata yin magana da kowacce kalma sai ta Alqur'ani.

Tsoron Allah shine zai sanya ka rika jin bakin ciki da damuwa acikin zuciyarka idan ka rasa Jam'in sallah sau 'daya rak!

Tsoron Allah shine zai sanya idan kana azumi, yadda bakinka ya kaurace ma abinci, hakanan dukkan gabobin jikinka zasu kaurace ma dukkan wani nau'i na sa'bon Allah.

Tsoron Allah shi zai sa ka nemi yafewar dan uwanka wanda ka zalunceshi acikin magana ko aiki.

Tsoron Allah shi zai barci ya gagareka saboda tunanin wani mummunan abu da ka aikata yanzu ko tun da dadewa.

Tsoron Allah shi zai sa ka rika runtse idonka daga kallon matar da bata halatta gareka ba. Kuma shi zai sa ka kauce daga kadaituwa da budurwarka, koda ka biya sadakinta... In dai ba'a daura aurenku ba.

Tsoron Allah shi zai sa ki tuba daga sanya matsatsun sutura, Shi zai sa ki dena nuna tsaraicinki koda atsakanin 'yan uwanki mata, ballantana a inda maza zasu iya kallonki.

Tsoron Allah shi zai sa kullum ka rika kauce ma bin son zuciyarka na sha'awa ko son tara abin duniya.

Tsoron Allah shi zai sa ka rika tsarkake zuciyarka acikin dukkan abinda zakayi

Nura Ashiru twd

AN  RUWAITO  ACIKIN  HADISI __________________________________________________Duk wanda ya ke wulakanta Sallah To Allah ...
28/10/2024

AN RUWAITO ACIKIN HADISI __________________________________________________
Duk wanda ya ke wulakanta Sallah To Allah zeyi masa ukuba guda goma Sha biyar (15)

• Guda biyar (5) Anan duniya

• Guda uku (3) Alokacin mutuwarsa

• Guda uku (3) Acikin kabarinsa

• Guda uku (3) Lokacin fitowarsa daga kabarinsa.


1. Za'a ɗebe Albarka A rayuwarsa
2. Za'a gusar da K**a ta mutanen kwarai a fuskarsa
3. Dukkanin wani aiki da zai aikata Allah bazai bashi ladaba
4. baza'a ɗaukaka addu'ar sa zuwa samaba
5. Baya daga cikin addu'ar salihan bayi


1. Zai mutu matsiyaci
2. Zai mutu yanajin yunwa
3. Zai mutu yanajin kishi.

• Kuma Koda za'a bashi ruwan koramun duniyar nan bazai masa maganin kishinba.


1. Za'a ƙuntata masa A kabarinsa har sai haƙar karinsa ya haɗe da ɗaya ɓarin haƙarkarin

2. Za'a sakamasa garwashin wuta Acikin ƙabarinsa yayi ta juyawa aciki dare da rana.

3. Za'a sako masa wata macijiya Acikin ƙabarinsa Mai suna (SHUJA'UL AQRA U) Daga cikin macizan wuta idanunta na wutane farcenta Kuma na baƙin karfene tsawon farcenta ɗaya tsawon tafiyar wuni ɗaya ne
Zata yiwa mamaci magana, maganarta kamar tsawa take zatace : Ubangijina ya umarceni Danai ta saranka tun lokacin sallar safiya har azahar, Daga sallar azahar har la'asar Daga sallar la'asar har magariba Daga sallar magariba har Isha'i Daga sallar Isha'i har safiya

Duk Sara ɗaya zai nutsa cikin kasa Ana yimai azaba har bazai gushe Anayimasa irin waɗannan azaba har tashin kiyama.


1. Hisabi Mai tsanani
2. Fushin ubangiji
3. Shiga wuta

Inna lillahi wa Inna ilaihi Rani'un
Allah ya bamu Ikon kiyaye sallah....Ameen

Don Allah idan ka karanta katurawa yan uwa da Abokai don su fadaka.

Kasani Manzon Allah (ﷺ) yace mutum ɗaya ya samu shiriya ta dalilinka yafi abaka jajayen rakuma.

Karka gajiya wajen yiwa Addininka hidma K**ar yadda wannan karatu ya isa gareka kaima isardashi zuwaga wasu.

Ya Allah idan lokacin muturmu tayi kasa mu cika muna masu imani 🤲🤲
NURA ASHIRU TWD

ALLAH SHI NE MAI YI.-"A rayuwa kada ka taba jin cewa wai don wani ya cire hanunsa a rayuwarka ko a wani abu da yake yi m...
25/10/2024

ALLAH SHI NE MAI YI.
-
"A rayuwa kada ka taba jin cewa wai don wani ya cire hanunsa a rayuwarka ko a wani abu da yake yi maka zaka tagayyara, hakika Allah shi ne mai yi, kuma kaima ba mantawa yayi dakai ba. don haka wani ya daina jin cewa idan babu shi to wani zai tozarta a rayuwa, idan ya cire hanunsa a cikin rayuwar wani zai wulakanta, lallai ne Allah shi ne mafi kyawun masu kula da bayi"
-
"Daga cikin kuskuren da za ka yi a rayuwa shi ne: kace ka janye hanunka ko taimakonka a kan wa'ne wai don yayi maka wani abu ba dai dai ba, don yayi maka wani ɗan ƙaramin laifi, baka sani ba watakila ma dominsa ne Allah yake ɗaukaka darajar dukiyarka"
-
"Watakila daga lokacin da kace ka daina taimaka masa, dai kaga albarkar dukiyar taka ta fara raguwa, wala-Allah daman Allah yana sawa dukiyar albarka ne sabida kana taimakonsa, to da ka janye masa tallafi sai shima Allah ya janyewa dukiyar taka nasa tallafin"

By Nura Ashiru twd ✍🏻

Ita rayuwa a yau zaka iya ganin wani mutum da baya da komai a yau, da kyar yake samun abinda zai ci b***e sutura b***e k...
22/10/2024

Ita rayuwa a yau zaka iya ganin wani mutum da baya da komai a yau, da kyar yake samun abinda zai ci b***e sutura b***e kayan more rayuwa duk baya dasu a yau, hatta fatar jikin sa zaka ga ta canza saboda jarabawar rayuwa da yake ciki, ba haka yaso ba, amma Qaddarar Ubangiji ne akan sa dole ya hakura ya karbi abinda aka hukunta masa.
~ Amma idan lokacin da Allah ya rubuta sauki zai zo masa sai kaga mutane sun dawo suna neman taimako wajen sa. Wanda ba kowa ba a yau shine wani a gobe.

Dan haka kada ka wulakanta wani mutum saboda ka fishi a yau, gobe lamarin zai iya canzawa. Rayuwa kamar Damina ce, baka da tabbacin gobe za'a yi ruwa ko ba za'a yi ba, baka sani ba gari zai yi sanyi ne ko zafi zai yi.
~ Mutane da yawa s**an raina wasu mutane, s**an wulakanta wasu mutane saboda basu da komai jiya, yau kuma hukuncin Allah ya canza.

~ Duk wanda kake tare dashi ka rike shi da mutunci da da daraja, kada ka bari sai Allah yayi masa budi ka dawo wajen sa. Nan da shekaru masu zuwa mutane ba zasu iya tuna kala ko launin rigar daka sanya a yau ba, amma zasu iya tuna kalar yadda ka mu'amalance a shekarun baya a lokacin da basu da komai.

~ Wannan daukaka da kake da ita a yau, gobe Allah zai iya bayar da ita ga wanda kake ganin ba kowa bane shi a yau. Ilimi ko damar da kake dasu a yau gobe za'a iya bayar da ninkin su ga wanda kake ganin baya da komai a yau domin abubuwan a hannun Allah suke, mutane basu iya sarrafa komai sai abinda Allah ya amince ya hukunta akan bayin sa..Allah katabbatar da duga duganmu Akan Sunnar Manzon Allah sallallahu alaihi wasallam ka nisantamu da ga dukkan bid.a babba koqarama achikin addininka🙏🥰
BY NURA ASHIRU TWD

Maza don Allah kuji tausayin mace.Maza don Allah ku tausayawa wa raunin mace.Maza don Allah ku girmama mace.Maza ku kall...
19/10/2024

Maza don Allah kuji tausayin mace.
Maza don Allah ku tausayawa wa raunin mace.
Maza don Allah ku girmama mace.
Maza ku kalli mace da mutunci.
Maza ku kalli sadaukarwa da mace takeyi.
Maza karku mayar da mace abar banza.
Maza ku duba wahalar da mace take sha,tun daga haihuwa,raino,har zuwa girman ku.

Maza ku kalli mace a matsayin mai daraja a gare ku,mace uwa ce gare ku,kuna kallon yadda mace take kulawa da 'yayanta duk yawan ku mace uwa bazata taba gazawa da ku ba.
Mace uwa ce wanda hawaye bai cancanci zuba daga idon ta ba,wato hawayen bakin ciki illa hawayen farin ciki daga idon ta.

Idan kuka duba mace raunin ta daban yake,abu kaɗan zai saka ta kuka,abu kaɗan za'a mata zata ga tamkar an musguna mata ne, hakuri da jurewa zakuna yi akan mace, saboda farin cikin ta na wajan ku,duk rayuwar mace yana karewa ne daga karkashin Namiji ne.

Tayi rayuwa da mahaifin ta.
Tayi rayuwa da mijin ta.
A karshe tayi rayuwa a karkashin yaron ta.
Ku dinga bata kulawa da nuna soyayyah.
By Nura Ashiru twd

Farin Ciki Yakan Ziyarce ni 🕺Aduk SandaNATUNA Cewa Ni MUSULMINE👳‍♀️KUMA AHALUSUNNAH 🥰 Bacin Rai 😭Yakan Ziyarce ni Aduk S...
18/10/2024

Farin Ciki Yakan Ziyarce ni 🕺Aduk Sanda
NATUNA Cewa Ni MUSULMINE👳‍♀️KUMA AHALUSUNNAH 🥰 Bacin Rai 😭Yakan Ziyarce ni Aduk Sanda NATUNA Cewa Ni Mai Yawan Laifine😭
Damuwa Takan Zomin Ina Tuna Mizan Tarar dashi Akbarina Basaniba
Nakan Zubar da Hawaye Na Aduk Sanda NATUNA Cewa Zan hadu da Mahaliccina Nasani Cewa Zai Tambayeni Taya Nagudanar Da Rayuwata Aduniya NIKUMA gashi Kullun ABUBUWAN sai karuwa sukeyi Yau niyi wanchan gobe nayi wannan Innah nillahi wah Innah ilaihin Raji'unh
Yah kakarbi Rayuwarmu Muna musulmai Kuma muminnai
Yah ka kyautata Ayukanmu
Yah Ka karbi ibadummu
Yah kabamu ikon Sada Zumunta
Yah Kabamu ikon Kyautatawa Junanmu da Alheri ALLAH kabamu Lfy da zaman Lfy ALLAH kabamu ikon Yin biyaya Ga iyayenmu mallammanmu abokan iyayenmu Yah Allah kakara Daga darajar musulunci da musulmai Wadanda Basada Lfy maza da tama yara da manya Allah kabasu Lfy Wadanda S**a Rigamu Gidan Gaskiya Allah kayi musu Rahama Ni sani ahalusunnah Ina yiwa Dukkanin Musulmai FATAN Alheri Allah KASA Muyi Karshen Kwarai.
By nura Ashiru twd

*Ki daina ganin namiji bai isa dake ba.**Ki daina yarda ana fada miki cewa duk abinda namiji yayi kema zaki iya yi.**Kar...
18/10/2024

*Ki daina ganin namiji bai isa dake ba.*
*Ki daina yarda ana fada miki cewa duk abinda namiji yayi kema zaki iya yi.*
*Karki yarda a zuga ki a akan* *kar kiyi biyayya ga namiji.*
*Karki raina namiji.*
*Karki saka kanki a irin* *wadanan matan da basu san* *kimar namiji ba*
*Karki yarda ki zama mai* *wulakanta namiji a rayuwar ki.*
*Namiji gata ne a gare ki.*
*Namiji jigo ne a rayuwar ki.*
*Namiji garkuwa ne a wajan ki.*
*Namiji rufin asirin ki ne.*

*Da yawa ana yiwa wasu matan wani hudubar da sam bai dace ba,ana zuga su ana nuna masu Rashin ganin* *girman namiji, irin wadannan matan ki nisance su,ba* *mutanan kirki ba ne za su hallaka ki,idan har kika bi wannan dabi'ar na su.*
*Idan kin lura irin wannan matan su babu ilimin addini a tare dasu,sun fi mayar da hankalin su ga bin tafarkin yahudawa.*

*Ki dinga tuna makomar ki a wajan Ubangiji.*
By Nura Ashiru twd

MACE...!An tambayi wani mai hikima dangane da mace sai ya bada amsa.Idan mace ma'abociyar (addini)ce to tanada daraja =1...
18/10/2024

MACE...!

An tambayi wani mai hikima dangane da mace sai ya bada amsa.

Idan mace ma'abociyar (addini)ce to tanada daraja =1

Idan tazama mai (kyau) sai akara sifili(0)tazama tana da =10

Idan tazama mai (dukiya)sai akara mata sifili(0) tazama=100

Idan tazama mai (nasaba)sai akara mata sifili(0) tazama tana da 1000

Amman idan ta rasa guda dayan farko wato (addini)sai acire (1)sai yaxama ba abunda yarage sai sifilai=000

Dan haka bata da komai na kima da daraja tarasa duk wani abu da zai mata ado da gata a duniya da lahira.

Ki yi ado da addini da dabi'a idan kika rasasu kin zama fanko babu abinda yayi saura.
By nura Ashiru twd

*KU KOYAWA YARANKU HALAYE UKU*:1. Yawan gaishe da na gaba dasu.2. Nutsuwa da barin wasa ahanya.3. Futa cikin kyakykyawar...
18/10/2024

*KU KOYAWA YARANKU HALAYE UKU*:
1. Yawan gaishe da na gaba dasu.
2. Nutsuwa da barin wasa ahanya.
3. Futa cikin kyakykyawar shiga.

*KU HANA YARANKU HALAYEN NAN*:
1. Yawan yawace-yawace.
2. Yawan Abokai/kawaye barkatai.
3. Rashin kunya da fadace-faface.

*KU RIKA GWABE BAKIN YARANKU*:
1. Idan suna sa baki a maganar manya
2. Idan suna kawo tsegumi da gulma.
3. Idan suna zagi ko karyata manya.

*KUYI MUSU HORO ME TSANANI*:
1. Idan suna wasa da Sallah.
2. Idan s**a fara kwadayi da roko
3. Idan s**a fara karya da lalaci.

*KU KARA JAWO YARANKU JIKI*:
1. Idan s**a balaga.
2. Idan basu da lafiya.
3. Idan kuna gida a zaune.

*KU KWADAITAR DA YARANKU*:
1. Nacin karatu da rubutu.
2. Dagewa wajen cimma buri.
3. Lada da nasara in anbi hanyar Allah.

*KU NUNAWA YARA MUHIMMANCIN*:
1. Riko da Addinin musulunchi.
2. Zumunchi da ziyarar dangi.
3. Lafiya, Lokachi da chance/kuruciya.

*KU DAINA WADANNAN AGABANSU*:
1. Bayyana tsiraici/mu'amalar aure
2. Wasan banza na kuruciya, kallo.
3. Bayyana rashin jituwa atsakaninku.

*KU YAWAITA AGABAN YARANKU*:
1. Karatun Alqur'ani da salloli.
2. Aikata gaskiya da Rukon Amana.
3. Wadatar zuci da godiyar Allah.

*SUKE JIN TSORON KU TA HANYAR*:
1. Tsawatar musu in sunzo da wargi.
2. Rashin barinsu babu abinyi.
3. Taqaita nuna musu so kuru-kuru.

*KU DAGE KU CIREWA YARANKU*:
1. Tsoron mutuwa.
2. Tsoron talauchi.
3. Tsoron wanda baya tsoron Allah.

*KU GOYI BAYAN YARANKU INHAR*:
1. sune ke da gaskiya.
2. Ba sa6o s**a aikata ba.
3. sunyi abu domin kare mutuncinku.

*KUKE TSORATAR DA YARANKU*:
1. Illar Hadama.
2. Futinar rigima.
3. Hadarin taqama da girman kai.

*KU RIKA SANARDA YARANKU*:
1. Asali da Tarihi.
2. Mutuwa da kabari.
3. Dadi da rashin sa.

*KU BAWA YARANKU HORO NA*:
1. Taqaita cin abinchi.
2. Karancin Barchi da zaman hira.
3. Watsarda dogon buri da sharholiya.
Allah yasa idan munji muyi aiki da abinda muka saurara ameen ya hayyu ya qayyum 🙏BY NURA ASHIRU TWD

Address

Kano
700103

Telephone

+2347071582194

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NURA ASHIRUGRAPHICSDesign posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to NURA ASHIRUGRAPHICSDesign:

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram