01/02/2026
"Bana fatan ko makiyina Allah ya jarabce shi da rashin haihuwa"
Daga Ciki da Raino
Mijina na biyu shekararsa 20 da auren farko amma cikin nufin ubangiji bai taba haihuwa ba, yayi aure har sau biyu, amma ba wadda ta taba yin ko da batan wata ballatana ta samun ciki a cikin matansa.
Allah mai yadda ya so, haka kaddarar mutuwar miji ta fito dani zawarci daga gidan tsohon mijina ina da 'yata daya da shi. Da yake mijina na biyun makocinmu ne, nan take ya nuna yana sona da aure. Yan uwana s**a bani shawarar na aure shi, tun da na yadda ina sonsa.
Bayan aurenmu da wata uku, ai kuwa sai gashi Allah ya bani ciki a gidansa. Murna kamar ya hau sama ya fado. Nan take ya haneni da kar na sanar da kowa wannan alkhairin har sai ya girma. Na ce masa to, amma ya kamata muje asibiti a duba lafiyar cikin, kamin mu fara zuwa ANC.
Domin a baya kaji abin da ya faru dani. A baya na samu matsalar ciki a wajen mahaifa, wanda ala tilas aka cire min hannun mahaifa daya, domin ceto rayuwata. To daga baya Allah ya kara bani wani cikin, kuma muka kula da lafiyar cikin ta mutunta ka'idoji da shawarwarin likita. Har Allah ya sauke ni lafiya, na haifi yata mace kyakkyawa.
Ya ce ba wata matsala, kowa da irin kaddararsa, wannan lafiya lau yake insha Allahu. Da sannu ciki har ya fara girma, gari kowa ma ya sani cewa na samu ciki. Akai tai masa murna.
Amma idan nai masa maganar zuwa awo, sai ya ce min in kwantar da hankalina, lafiya lau zan haihu domin bana son a mai da min dana dan kwaya tun yana cikin mahaifa. Maganganunsa sunyi tasiri a kaina, har nake gani lallai ba makawa haka abin ya ke.
In takaita muku zance, karshe dai tiyata na kare, sakamakon ciwon jijjiga da nayi. Jaririn ma bai yi ko minti 10 ba, da fitowa duniya yace ga garinku nan. Shima yaron kyakkyawa dashi gashi idan ka ganshi sak mahaifinsa ya biyo shu sosai, musamman a fuskarsa da karan hancinsa ๐ญ๐ญ.
Tun daga wancan lokaci har zuwa yau din nan da nake baku labari ban sake samun ciki ba.
Yau gashi shekararta 7 kenan da aurenmu, har yanzu ko batan wata ban sake yi ba.
Mijina yayi matukar nadamar kuskuren da ya aikata akan kin amincewa da fara zuwa asibiti tun da wurwuri tare domin fara awo (ANC).
Ku sanya mu a addu'o'inku, Allah ya duba lamarinmu, ya bamu masu albarka idan muna da rabo ๐ญ๐ญ๐ญ. Dama sauran masu nema.
Shawarata, don Allah mazaje ku dinga turawa tare da takurawa matanku zuwa AWON CIKI domin akwai falala mai yawa a cikinsa.
Ku taya mu yadawa domin wasu suma su amfana.