01/03/2026
KO KASAN SIRRIN ADDU'A ?
Rubutawa cibiyar
👇👇
Kowace cuta da maganinta
Da sunan Allah mai Rahma mai jinkai.
Addu'a maganice ga dukkanin kowace irin bukata ta duniya da lahira,kama daga neman lafiya,arziki,daukaka,ilmi,cin galaba,samun kariya daga abokan gaba,neman haihuwa,neman mulki da soyayyar jama'a,da dai makamantansu.
Allah (swt) yana cewa "ku rokeni zan amsa muku,lallai wadanda suke yin girman kai wajen bauta (addu'a) za su shi ga jahannama suna kaskantattu"
2.Allah (swt) ya ce "kace musu ubangijina ba ruwansa daku ba don rokonsa da ku keyi ba."
3.Allah (swt) yace " idan bayina sun tambayeki game dani ka ce musu ina kusa dasu,ina amsa addu'ar mai addu'a idan yayita.
4.Annabi (.s.a.w) "yace duk wanda baya rokon Allah,Allah zai yi fushi da shi".
5.Annabi (s.a.w) yace "ba'a maida addu'ar da akayita tsakanin kiran sallah da tada iqama"
6.Annabi (s.a.w) ya ce "ana amsa addu'ar dayanku matukar bai yi gaggawa ba ya na cewa ni na roki Allah amma har yanzu bai amsa min ba."
Dan-adam ya cika gaggawa,mun fi bukatar da zaran mun roka sai a bamu nan take,wanda bahaka bane,addu'a dagewa take so,kada a ja baya,kar mu yi sanyi a guiwa wallahi za a samu biyan bukata.
7.Annabi (s.a.w) ya ce "duk wanda ya tashi daga bacci a cikin dare ya ce "LA'ILAHA ILLALLAHU WAHDAHU LASHARIKALAHU,LAHUL MULKU WALAHUL HAMDU WAHUWA ALA KULLI SHAI'IN QADIR,SUBHANALLAH,WALHAMDULILLAH,WALAILAHA ILLALLAHU WALLAHU AKBAR,WALAHAULA WALAQUWATA ILLA BILLAH,RABBI GIFIRLI,Annabi S.AW yace "za'a gafarta maka,idan kai addu'a za'a karba maka,in kai sallah za'a amsa maka.
8.Annabi (s.a.w) yace "Ana karbar addu'ar wanda yake cikin tsanani da kuma wanda yake a cikin tafiya"
9.Annabi s.a.w ya ce " cin haramun yana hana karbar addu'a."
ka ci haram,ka sha haram,ka sanya haram,kuma kace ka yi addu'a Allah ya amsa maka ?
10.Dukkan Annabawai dan za su yi addu'a,suna rokon Allah da sunan "YA RABBI" Kamar yanda Qur'ani mai girma ya nuna
11.Anso idan mutum zai yi addu'a sai ya fara godewa Allah kan ni'im