11/02/2026
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.
Cikin alhini da juyayi nake sanar da rasuwar baiwar Allah marainiya, wacce muka nema mata taimakon jinya, mai suna Suwaiba Ishaq.
Yan’uwanta sun sanar da ni rasuwarta a jiya da la’asar.
Muna roƙon Allah (SWT) Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kurakuranta, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zama makomarta tare da sauran Musulmi baki ɗaya. Ameen.
Allah Ya sanya jinyar da ta sha ta zama kaffara a gare ta, Ya sa ta huta daga wahala, Ya kwantar da ita a dausayin Aljannah. 🤲
Haka kuma, duk wanda ya taimaka domin a ceci rayuwarta, ko da addu’a ne ko dukiya ko ƙoƙari, Allah Ya saka musu da alheri, Ya biya musu bukatunsu, Ya saka musu da gidan Aljannah. Ameen.
Allah Ya ba iyalanta da ’yan’uwanta da duk masu kaunarta haƙurin jure wannan rashi. Ameen.