30/12/2025
HAR YAU BA MU SAMU GWARZON DA LABARIN SIRRI NA KISA BAI FIRGITA BA KAMAR SARDAUNA, YA LURA DA SHIRIN KISAN GILLA NA NZEOGWU AMMA YA ZAUNA DON AMANAR AL’UMMA DA YA DAUKA
NZEOGWU YA KIRKIRO ZARGIN CEWA SARDAUNA YA SHIGO DA MAKAMAI DAGA KASASHEN LARABAWA DON YIN JIHADI!
MASU RURA WUTAR KABILANCI A AREWA ALMAJIRAN NZEOGWU NE KUMA ‘YAN BARANDAN NNAMDI KANU
Duk gagaruman nasarori da Gamji mazan kwarai Sir Ahmadu Bello ya cimma tun daga haihuwarsa a Rabah har zuwa yi ma sa kisan gilla a gidan Arewa da ke Kaduna shekaru 56 ne kacal. Hakika Sardauna ya fahimci take-taken Chukwuma Nzeogwu na shirin kisan gilla amma bai yi ko gezau ba. Gwamnan kudu maso yamma Sir Ladoke Akintola ya zo Kaduna don shawartar Gamji cewa su fice daga kasar don gudun mutuwa amma Sardauna sam bai amince ba don shi a wajensa al’umma ta ba shi amana, don haka sai bayan ransa amma ba zai gudu ya bar al’umma ba. Bai tara zinari ba b***e azurfa kuma hatta rigunan Sardauna ma an san yawansu. A nan Sardauna bai tauyewa Ladoke Akintola hakki ba don ya ce in ya na son guduwa zai iya yin hakan. Nan fa Akintola ya juya ya koma Ibadan inda a nan ne miyagu su ka yi ma sa kisan gilla rana daya da su ka kashe Sardauna da Sir Abubakar Tafawa Balewa wato 15 ga Janairu 1966.
Bayan kisan gilla ga Sardauna akwai jami’an da su ka buya don gudun zaluncin rundunar Nzeogwu. Marigayi ministan Ilimi Wazirin Katsina Alhaji Isa Kaita ya shaidawa Sheikh Abubakar Gumi labarin juyin mulkin da sojoji su ka yi kuma ya bukaci ya tafi gidan Firimiya don duba abun da ya wakana. Nan Sheikh Gumi ya yi sallar asuba ya kuma k**a hanya sai gidan Arewa ya tarar da ko ina ya turnuke da hayaki don an yi amfani da manyan mak**ai wajen farmakin, ga sojoji nan da can rike da bindigogi, ya kutsa kai cikin gidan ya tarar da gawar Sardauna cikin jini a nan inda a ke tsayar da motoci. An kashe Sardauna da matarsa Hafsa. Nan Sheikh Gumi ya ce a kai marigayan gidan sarkin musulmi a nan anguwar Sarki inda a ka shirya su kuma Sheikh ya yi mu su sallar jana’iza. Allahu Akbar Sheikh Gumi jan gwarzo ne da masu kisan gilla ba su sa ya raurawa ba.
A ranar aiki, Sheikh Gumi na ofishinsa sai Nzeogwu ya turo sojoji su ka dauke shi zuwa wajensa. Nan ya tari Sardauna cikin murmushin jin dadin ya kashe Sardauna. Nan ya tambayi Sheikh Gumi inda su ka kai mak**an da su ka shigo da su daga ketare don yin jihadi. Sheikh Gumi cikin al’ajabi don ya yi tsammanin ko Nzeogwu zai yi ma sa ta’aziyya ne duk da dama ba ya tsammanin nadama daga wajen mugun maciyin amana dan ruruta yakin kabilanci. Sheikh Gumi ya nemi karin bayanin abun da Nzeogwu ke nufi. Nan Nzeogwu ya ce sun samu labarin Sardauna ya shigo da mak**ai daga kasashen Larabawa don yaki da duk wadanda ba musulmi ba ta hanyar kaddamar da jihadi. Nan Sheikh Gumi ya ce ma sa a wajensa ya fara jin labarin nan kuma duk ziyarar Sardauna kasashen Larabawa tare su ke tafiya a matsayinsa na mai ba shi shawara kan lamuran musulunci kuma ba inda a ka taba irin wannan mummunar magana watsatstsiya.
A nan Sheikh Gumi ya fahimci kirkire-kirkiren karya na zargin musulmi za su kai wa wadanda ba musulmi ba hari, su ka haddasa kisan gilla ga Sardauna. Hakika daya dalilin na zahiri shi ne fifita al’ummar Arewa da Gamji ya yi don karfafa su, su ilmantu da kula da Lardinsu don kar su zama ‘yan kallo a kasa. Har yau wannan alherin na Sardauna duk ‘yan Arewa ke amfana da shi ciki kuwa har da ‘yan barandan IPOB masu son kunna wutar fitina a Arewa don hakan ya ba da damar kafa Biyafara da kasar kabilanci ta MIDDLE BELT. Manjo Gideon Orkar ya so farfado da wannan mummunar kiyayya ta karya lokacin da ya yi yunkurin kifar da gwamnatin Janar Babangida a 1992 ya kori jihohin da ba na ikirarin yankin MIDDLE BELT ba daga Najeriya. Su Orkar sun yi nasarar zubar da jinin dogarin Janar Babanbida wato Laftanar Kanar UK Bello.
Duk makiyin Shehu Mujaddadi na kammala aikin Turawan mulkin mallaka ne na yaki da tasirin musulunci. Sammakal ne makiya Sardauna na koyi ne da karyar da Nzeogwu ya hau kan ta wai Sardauna ya shigo da mak**ai daga kasashen Larabawa don yaki da wadanda ba musulmi ba wai Sardauna zai yi jihadi!.
Miyagun iri ba za ku yi nasara ba, Turawa sun gwada har da datse kan Sultan Attahiru sun gaza. Nzeogwu ya harbe Sardauna bisa doron karya ya gaza. Gideon Orkar ya kori jihohin wadanda ya tsana daga Najeriya amma juyin mulkinsa ya juye kansa. Nnamdi Kanu ya yi ta zagin Najeriya da zayyana ta da gandun adana dabbobin daji amma yau ya na gidan yari. Yo dakkan shaidanu ma ba su cimma buri ba b***e tarkace ‘yan baranda masu buya a wayar salula ba hoto ba sunan gaskiya. Kul
Nasiru Adamu El-hikaya