Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.

Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. AN BUDE WANNAN SHAFI NE,SABODA TUNATAR DA KAWUKAN MU
BISA KYAWAWAN AL'ADUMMU NA HAUSA,

WADAN DA AYA Mungode

Dan Bunkasa Harshen Hausa da Al'adunsa,
Muna Maraba da shawarwarinku Domin wannan shafi naku ne.

HAR YAU BA MU SAMU GWARZON DA LABARIN SIRRI NA KISA BAI FIRGITA BA KAMAR SARDAUNA, YA LURA DA SHIRIN KISAN GILLA NA NZEO...
30/12/2025

HAR YAU BA MU SAMU GWARZON DA LABARIN SIRRI NA KISA BAI FIRGITA BA KAMAR SARDAUNA, YA LURA DA SHIRIN KISAN GILLA NA NZEOGWU AMMA YA ZAUNA DON AMANAR AL’UMMA DA YA DAUKA

NZEOGWU YA KIRKIRO ZARGIN CEWA SARDAUNA YA SHIGO DA MAKAMAI DAGA KASASHEN LARABAWA DON YIN JIHADI!

MASU RURA WUTAR KABILANCI A AREWA ALMAJIRAN NZEOGWU NE KUMA ‘YAN BARANDAN NNAMDI KANU

Duk gagaruman nasarori da Gamji mazan kwarai Sir Ahmadu Bello ya cimma tun daga haihuwarsa a Rabah har zuwa yi ma sa kisan gilla a gidan Arewa da ke Kaduna shekaru 56 ne kacal. Hakika Sardauna ya fahimci take-taken Chukwuma Nzeogwu na shirin kisan gilla amma bai yi ko gezau ba. Gwamnan kudu maso yamma Sir Ladoke Akintola ya zo Kaduna don shawartar Gamji cewa su fice daga kasar don gudun mutuwa amma Sardauna sam bai amince ba don shi a wajensa al’umma ta ba shi amana, don haka sai bayan ransa amma ba zai gudu ya bar al’umma ba. Bai tara zinari ba b***e azurfa kuma hatta rigunan Sardauna ma an san yawansu. A nan Sardauna bai tauyewa Ladoke Akintola hakki ba don ya ce in ya na son guduwa zai iya yin hakan. Nan fa Akintola ya juya ya koma Ibadan inda a nan ne miyagu su ka yi ma sa kisan gilla rana daya da su ka kashe Sardauna da Sir Abubakar Tafawa Balewa wato 15 ga Janairu 1966.

Bayan kisan gilla ga Sardauna akwai jami’an da su ka buya don gudun zaluncin rundunar Nzeogwu. Marigayi ministan Ilimi Wazirin Katsina Alhaji Isa Kaita ya shaidawa Sheikh Abubakar Gumi labarin juyin mulkin da sojoji su ka yi kuma ya bukaci ya tafi gidan Firimiya don duba abun da ya wakana. Nan Sheikh Gumi ya yi sallar asuba ya kuma k**a hanya sai gidan Arewa ya tarar da ko ina ya turnuke da hayaki don an yi amfani da manyan mak**ai wajen farmakin, ga sojoji nan da can rike da bindigogi, ya kutsa kai cikin gidan ya tarar da gawar Sardauna cikin jini a nan inda a ke tsayar da motoci. An kashe Sardauna da matarsa Hafsa. Nan Sheikh Gumi ya ce a kai marigayan gidan sarkin musulmi a nan anguwar Sarki inda a ka shirya su kuma Sheikh ya yi mu su sallar jana’iza. Allahu Akbar Sheikh Gumi jan gwarzo ne da masu kisan gilla ba su sa ya raurawa ba.

A ranar aiki, Sheikh Gumi na ofishinsa sai Nzeogwu ya turo sojoji su ka dauke shi zuwa wajensa. Nan ya tari Sardauna cikin murmushin jin dadin ya kashe Sardauna. Nan ya tambayi Sheikh Gumi inda su ka kai mak**an da su ka shigo da su daga ketare don yin jihadi. Sheikh Gumi cikin al’ajabi don ya yi tsammanin ko Nzeogwu zai yi ma sa ta’aziyya ne duk da dama ba ya tsammanin nadama daga wajen mugun maciyin amana dan ruruta yakin kabilanci. Sheikh Gumi ya nemi karin bayanin abun da Nzeogwu ke nufi. Nan Nzeogwu ya ce sun samu labarin Sardauna ya shigo da mak**ai daga kasashen Larabawa don yaki da duk wadanda ba musulmi ba ta hanyar kaddamar da jihadi. Nan Sheikh Gumi ya ce ma sa a wajensa ya fara jin labarin nan kuma duk ziyarar Sardauna kasashen Larabawa tare su ke tafiya a matsayinsa na mai ba shi shawara kan lamuran musulunci kuma ba inda a ka taba irin wannan mummunar magana watsatstsiya.

A nan Sheikh Gumi ya fahimci kirkire-kirkiren karya na zargin musulmi za su kai wa wadanda ba musulmi ba hari, su ka haddasa kisan gilla ga Sardauna. Hakika daya dalilin na zahiri shi ne fifita al’ummar Arewa da Gamji ya yi don karfafa su, su ilmantu da kula da Lardinsu don kar su zama ‘yan kallo a kasa. Har yau wannan alherin na Sardauna duk ‘yan Arewa ke amfana da shi ciki kuwa har da ‘yan barandan IPOB masu son kunna wutar fitina a Arewa don hakan ya ba da damar kafa Biyafara da kasar kabilanci ta MIDDLE BELT. Manjo Gideon Orkar ya so farfado da wannan mummunar kiyayya ta karya lokacin da ya yi yunkurin kifar da gwamnatin Janar Babangida a 1992 ya kori jihohin da ba na ikirarin yankin MIDDLE BELT ba daga Najeriya. Su Orkar sun yi nasarar zubar da jinin dogarin Janar Babanbida wato Laftanar Kanar UK Bello.

Duk makiyin Shehu Mujaddadi na kammala aikin Turawan mulkin mallaka ne na yaki da tasirin musulunci. Sammakal ne makiya Sardauna na koyi ne da karyar da Nzeogwu ya hau kan ta wai Sardauna ya shigo da mak**ai daga kasashen Larabawa don yaki da wadanda ba musulmi ba wai Sardauna zai yi jihadi!.

Miyagun iri ba za ku yi nasara ba, Turawa sun gwada har da datse kan Sultan Attahiru sun gaza. Nzeogwu ya harbe Sardauna bisa doron karya ya gaza. Gideon Orkar ya kori jihohin wadanda ya tsana daga Najeriya amma juyin mulkinsa ya juye kansa. Nnamdi Kanu ya yi ta zagin Najeriya da zayyana ta da gandun adana dabbobin daji amma yau ya na gidan yari. Yo dakkan shaidanu ma ba su cimma buri ba b***e tarkace ‘yan baranda masu buya a wayar salula ba hoto ba sunan gaskiya. Kul

Nasiru Adamu El-hikaya

KOWANE TSUNTSU KUKAN GIDANSU YAKEYI Rubutawa: Abdullahi Hassan, Potiskum     Waka baiwa ce da Allah ya horewa wasu, wadd...
30/12/2025

KOWANE TSUNTSU KUKAN GIDANSU YAKEYI

Rubutawa: Abdullahi Hassan, Potiskum

Waka baiwa ce da Allah ya horewa wasu, wadda ke nuna hikimar iya tsarawa da rerawa. Tsawon tarihi da zamani, waka tana tafiya daidai da kowane lokaci da irin salon da yanayi ya bukata.

A adabin Larabci, ana raba mawaƙa ta hanyoyi daban-daban, amma rarrabuwa mafi shahara da sauƙin fahimta ita ce rabe-rabe guda huɗu: zamanin Jahiliyya, zamanin Musulunci, zamanin Umawiyya, da zamanin Abbasiyya.

Wannan rarrabuwa ba wai kawai ta dogara da lokaci ba, har ma tana bayyana yanayin tunani, akida, da manufar waƙa a kowane zamani.
Mawakan zamanin Jahiliyya sun shahara wajen rera waƙoƙin alfahari, jarumta, soyayya da yaƙi, abin da ya dace da rayuwar wancan lokaci mai cike da ƙabilanci, faɗa da girman kai. Daga cikin fitattun mawakan wannan zamani akwai: Imru’ul-Qais, Antara bn Shaddad, da Zuhair bn Abi Sulma. Duk lokacin da aka ambaci waɗannan sunaye, abu na farko da ke zuwa zuciya shi ne duhun jahiliyya da rayuwar da ba ta da hasken shiriya.
Da zuwan Musulunci kuma, waƙa ta samu sauyi mai girma, musamman a zamanin Annabi s,a,w, Mawakan wannan zamani sun mayar da hankalinsu wajen kare Musulunci, inganta ɗabi’a da tabbatar da tauhidi. Ba a yin waƙa sai wadda take da alaƙa da sakon Annabi s,a,w, da gina al’umma bisa gaskiya da imani. Daga cikin fitattun mawakan wannan zamani akwai Hassan bn Thabit da Ka‘ab bn Zuhair.

A wannan lokaci, ba a yarda a wake wani mutum saboda matsayi ko suna ba, kuma babu wani sahabi da ya kai matsayin da za a rera masa waƙa don girmamawa ko kare shi daga maƙiyansa.

A zamanin Umawiyya kuwa, lokacin mulkin Banu Umayyah, an sake ganin dawowar wani salo na jahiliyya, inda waƙa ta koma zagi da martani (naqā’iḍ), siyasa da ƙabilanci. A wannan zamani ne aka ga yaƙin kalmomi tsakanin mawaka, tare da yabon sarakuna da zambo ga abokan gaba. Fitattun mawakan wannan zamani sun haɗa da Jarir, Farazdaq, da Akhtal, waɗanda s**a yi fice wajen rigingimun waƙoƙi da nuna fifikon ƙabila da siyasa.

Zamanin Abbasiyya kuma ya zo ne da bunƙasar ilimi da adabi, lamarin da ya sa waƙa ta faɗaɗa zuwa fannoni da dama. Mawakan wannan zamani sun fi karkata zuwa hikima, falsafa, nishadi da soyayya, tare da zurfin tunani da ingantaccen salo. Daga cikin shahararrun mawakan wannan zamani akwai Abu Nuwas, Al-Mutanabbi da Abu Tammam.

A ƙarshe, wannan bayani yana nuni da cewa ana iya gane mawaƙi ne ta abin da yake wakewa da manufar waƙoƙinsa. Akwai mawaƙan addini, kuma akwai mawaƙan jahiliyya, kuma kowane nau’i yana bayyana ne ta ayyukansa. Waƙa, a kowane zamani, madubi ce da ke nuna halin da al’umma ke ciki da alkiblar tunaninta.

‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA NA KOKARIN BOYE ADDININSU DON YAUDARAR HAUSAWA, AMMA BA SA SAMUN NASARA SAM SAI TSILLI-TSILLI DA...
29/12/2025

‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA NA KOKARIN BOYE ADDININSU DON YAUDARAR HAUSAWA, AMMA BA SA SAMUN NASARA SAM SAI TSILLI-TSILLI DA IDANU

WANI TANTIRIN MAKARYACI YA CE MUSULUNCI YA YI SHEKARU 1460 A KASAR HAUSAWAN BOGI YAYIN HAIHUWAR MUJADDADI!

DAN KWANGILAR YA YI IKIRARIN ADDINI DA YA YI SHEKARU 280 GABANIN FARA WAHAYI SHEKARU 13 GABANIN HIJIRAR MANZON ALLAH SAW

Daga saka hula zuwa tsarin karin harshe da ma yawan ambata “MU” kaza da kaza na tabbatar da ‘yan karyar Hausa zalla ba su da alaka da Hausa hasalima makiya Hausawa ne kuma gaggan makiya addinin Hausawa. Me ma zai sa mutum ya bata lokaci ya na magana da sojojin ‘yan ta’addan Hauswan bogi na soshiyal midiya da ke boye ruff a wayar salula ba suna ba hoto sai izgilancin wai gwagwarmaya su ke yi! Yo an taba dan gwagwarmaya boyeyye matsoraci in ba a MIDDLE BELT ba. Kai ko ‘yan burbudi da ke gefen garuruwanmu na Katsina, Kano, Jigawa da Zamfara ‘yan banza bakwai ne na hakika don sun tsani kalmar shahada sun kuma tsani jin kiran sallah shi ya sa ma akasarinsu ke zama a kauyukan su-ya-su abu namu maganin a kwabe mu.

Na so yau ma na cigaba da tarihin ta’addancin da Turawan mulkin mallaka su ka yi a Arewacin Najeriya daga shigowarsu a 1903 ciki da wulakanta gawar Sultan Muhammad Attahiru bayan yi ma sa kisan gilla da tsayawa a fagen yaki su karisa kashe wadanda ba su gama cikawa ba su na gargara da furta kalmar shahada. Sai wani martani ya ja hankalina na daya daga ‘yan kwangilar Hausa zalla wanda mun dade mu na hulda shi tun kafin bayyanar wannan annamimancin Abdullahi Inuwa Gusau. Na sha jan hankalinsa ya bar wannan tafiya amma sam ya bijire har na fahimci biri ya yi k**a da mutum.

Abduulahi Gusau ya yi ikirarin cewa a lokacin da a ka haifi Mujaddadi Shehu Danfodio, addinin musulunci ya yi shekaru 1460 amma a kasarsu ta karyar Hausa zalla. Ban dau wannan martani da wasa ba don na ga abun ya shafi musulunci kuma har bayan sa’a 48 bai canja matsaya ba kuma da alamu hatta a zauren makircinsu na Whatsapp ba wanda ya ja hankalinsa cewa ya janye ikirarin. Na duba tarihi an haifi Shehu Mujaddadi a shekara ta 1754 milidiyya daidai da shekara ta 1167 hijiriyya. Manzon Allah ya yi shekaru 53 a Makkah gabanin hijra kuma shekaru 13 bayan wahayi. Don haka sai mu dauko farkon wahayi da kira zuwa musulunci shekaru 13 a hada su da shekaru 1167= 1180. Tantirin makaryaci Abdullahi Inuwa Gusau ya kirkiro wani addini kenan da ya yi shekaru 280 gabanin fara wahayi. Cikin sauki shekaru 1460-1180= 280. Kai wadannan mutanen ‘yan bazata ne ‘yan shigar burtu kuma ina kira da babbar murya a yi watsi da su.

Duk abun da Hausawan bogi ke fada karya ne. Sun ginu a kan karya kuma za su lalace a doron karya. Ba riba a duniya sai ta kulla makirci, in kuma su ka tafi lahira da kunna fitinar kabilanci za su gamu da Allah a madakata. Kuma yanda a ka dauko matakin murkushe ‘yan ta’addan daji da duk masu alaka da yi wa kasa zagon kasa, ‘yan ta’addan soshiyal midiya masu ruruta fitinar kabilanci da dinka rigar karya ta Hausawa su shafawa kan su ruwa don saura kiris a fara cafke su don fuskantar tuhumar cin amanar kasa. Ina mu su gargadi ne don akalla na ga su na ciccijewa da tsamin baki su na magana da harshen Hausa. Kun ga kuwa ai in mun ji mutum ya yi Hausa za mu kai ma sa agaji face in halinsa ya nuna makiri ne.

Nasiru Adamu El-hikaya

HATTA MULKIN MALLAKA A DAULAR SOKOTO TA HANNUN SARAKUNA, NA NUNA DARAJAR SHEHU MUJADDADIDUK MAI ZAGIN SHEHU ZA KA TARAR ...
27/12/2025

HATTA MULKIN MALLAKA A DAULAR SOKOTO TA HANNUN SARAKUNA, NA NUNA DARAJAR SHEHU MUJADDADI

DUK MAI ZAGIN SHEHU ZA KA TARAR KAN ADDININ MUSULUNCI NE, KUMA KA NA KARA BINCIKE ZA KA GANO DASHE NE MAKIYIN MUSULUNCI

SHEHU ADDINI YA KAFA SHI YA SA HAR GOBE DAULARSA KE BIN MUSULUNCI DON HAKA DAULAR NA NAN DARAM A MASALLATAI DA MAKARANTU DA ZUKATA

Gaggan Turawa wadanda ke kan gaba cikin wadanda su ka yi wa sassan Amurka mulkin mallaka gabanin kafata a 1776 wato ‘yan Burtaniya, sun mika wuya ga Daular Sokoto ta Shehu Mujaddadi duk da kwace ikon Daular ta hanyar gwabza yaki. Don ganin tsarin shugabanci mai adalci na ilimi da musulunci mai tsabta, ba bori ba tsafi, sai su ka mulki Daular ta hanyar Sarakuna. Shugaban Amurka na farko da ya jagoranci rundunar juyin juya halin kwatar mulki daga Burtaniya George Washington na da shekaru 22 kacal a duniya a ka haifi Shehu Mujaddadi a 1754. Karankataf tsakanin kafa Amurka daga yankin nahiyar Amurka ta Arewa da Daular Sokoto ta Shehu shekaru 28 ne kacal. Yayinda George Washington ya bar duniya a 1799 ya na mai shekaru 67, Mujaddadi ya bar duniya a 1817 ya na mai shekaru 66. Sai bayan rasuwar Shehu da shekaru 86 a shekara ta 1903 Turwan mulkin mallaka na Burtaniya karkashin Gwamna Lugga wato Lord Luggard da kwamandan yaki Sir Thomas Morland su ka ci Daular Sokoto bayan faro farmaki daga Yola.

Kai Turawa sun sha mamaki don sun dauka za su zo su samu a na taka rawa da waka, mata da maza na iskanci, sai su ka yi turus da ganin mutane a natse cikin sutura mai kyau da tsarin karatu da karantarwa ga rangada kiran sallah sau 5 a kullum. Sun kara shan mamaki don Sultan na karshe na Daula Muhammad Attahiru ya ce faufau ba zai zauna karkashin mulkin kafurai ba kuma haka ya ki mika wuya su ka bi shi har Bormi a yankin jihar Gombe na zamanin yau su ka yi ma sa kisan gilla amma shi ma kwamandan Turawan Manjo Francis Charles Marsh ya sheka barzahu minti 20 kacal bayan harba ma sa wata kibiya daga dakarun Daula. Kabarin Sultan Attahiru da na Manjo Marsh duk na nan a Bormi kuma Turawan Burtaniya na zuwa ziyarar kwamandansu.

Duk Turawan nan sun amfana kwarai da ilimi a aikin da su ka yi na mulkin mallaka a Daular Sokoto don yanda a ka shunfuda tsarin shugabanci na adalci da ba a taba gani ba a tsakanin wadannan Daulolin na wannan zamani kuma da alamu har a busa kaho ba za a sake kafa Daular da za ta yi tasiri wajen gagarar Bature sauya ma ta salo irin Daular Shehu ba. Kai tsaye zan ce an ci Daular Shehu wajen kwace ragamar iko amma sam ba a ci Daular wajen koyarwa da bin tsarin musulunci ba. Shehu a shekarun da ya yi a duniya 63 kacal masu albarka amma ya bi koyarwar magabata tun daga tsarin karnonin al’ummar musulunci har zuwa ga Sahabban Manzon Allah mai tsira da aminci.

Gaskiyar magana har yau din nan da na ke rubutun nan, Daular Sokoto ta Shehu Mujaddadi na nan kan koyarwar Islama wacce dama asasin kafuwarta kenan don koyar da al’umma sahihiyar akidar musulunci ba shirka, ba bori ba tsafi ba camfe-camfen banza da wofi.

Allah madaukakin Sarki ya cikawa Shehu burinsa tun ya na raye na ganin al’umma ta hau saiti kan addinin musulunci don haka Turawa na zuwa su ka mika wuya duk da sun zo da addininsu na kiristanci kuma sun yi marmarin kowa ya zama kirista.

Zuwa yau shekaru 208 da wafatin Shehu amma KALIMATULLAHI HIYAL ULYA daga Sokoto har Maiduguri daga Ilori har Yola. To sai kaka kenan ‘yan kwangilar IPOB da sauran makiya Arewa?.

Kowa ya kwantar da hankalinsa don tabbas ba wani hari da zai wargaza musulunci a yankin Daular Shehu.

Nasiru Adamu El-hikaya

INA FATA DA MAGUZAWAN DA ABOKAN BURMINSU DUK KUN GANE SU A FARAFAGANDAR TSIYA TA KARYAR HAUSA ZALLAYanzu mun fara ma hut...
14/12/2025

INA FATA DA MAGUZAWAN DA ABOKAN BURMINSU DUK KUN GANE SU A FARAFAGANDAR TSIYA TA KARYAR HAUSA ZALLA

Yanzu mun fara ma hutawa da dogon bayani kan wadannan ‘yan kwangilar rusa Arewa da yaki da musulunci masu fakewa da kwatowa Hausawa hakki alhali Hausawan su ke yaka, addinin Hausawan da Arewar Hausawa. Haba ai ni daga ganin yanda su ke salon rubutu na san ba Hausawa ba ne kuma ba su da alaka da Hausawa ko ruhin addinin Hausawa.

Yanzu ma sun fito fili tarwal sun fara kalmomi na logar addininsu. Haba waye bai taba jin masu s**ar jihadin Manzon Allah mai tsira da aminci ba da cewa “in dai addinin Allah ne, me ya sa sai an taya Allah yaki, ai ya fi karfin kowa a bar ma sa addininsa ya yi yaki da wadanda su ka bijire ma sa” To kun gani hatta sallah da musulmi ke yi wasu na ganin ai ba dole sai mutum ya yi kullum ba don ai in Allah ya na da tausayi ba zai umurci bayinsa su rika shan wahala haka ba!. Mutanen nan ba su dauka Allah ya sauko da mutum doron kasa don ya yi ma sa jarrabawa ba ne in ya ci jarrabawa ya samu sak**ako mai kyau in kuma ya fadi jarrabawa ga tanadin wadanda su ka fadi jarrabawa ko da ta nan makarantar duniya akwai maimaita aji ko in ya yi tsanani ma a sallami dalibi.

Don haka ina ribar ‘yan karyar Hausa zalla su bijirewa kananan kabilun da yawancinsu Allah ya nufa a ciki a ka haife su, su ka yi wuf su ka karbo kwangilar makiya su ka dinka rigar karya a soshiyal midiya ba sunan gaskiya, ba adireshi ba hoto sai zagin Shehu Mujaddadi da yi wa musulunci habaici? Matsoratan banza.

In Allah ya yarda an jima kadan zai dawo da cikekken bayani.

Nasiru Adamu El-hikaya

HOTUNA DA ZAYYANE-ZAYYANE KADAI SUN ISA NUNAWA DUNIYA, YANDA ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA SU KA RAINA HAUSA DA HAUSAWA!BA HOT...
14/12/2025

HOTUNA DA ZAYYANE-ZAYYANE KADAI SUN ISA NUNAWA DUNIYA, YANDA ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA SU KA RAINA HAUSA DA HAUSAWA!

BA HOTUNAN ALLO A TSANGAYA NA KASAR HAUSA SAI KAYAN KIDA KAMAR KUNGIYAR DUJJAL

Ko gabanin na yi bincike kan miyagun mutane da ke ikirarin karya na Hausa zalla, na fahimci sun raina Hausa da Hausawa tun da ai ba harshensu ba ne kuma cigaban Hausawa ba damuwarsu ba ce. K**ar yanda masu hikima ke cewa in ka na son gane kowaye mutum to dubi waye abokinsa. Daga yanayin hotunan karya da zayyane-zayyane da miyagun ke kwatanta Bahaushe da su za ka gane irin mummunan hoton Hausawa da ke zuciyarsu.

Kowa ya duba zai ga kusan duk masu ruruta fitinar nan ta kabilanci ba hotonsu, ba sunan gaskiya ba adireshi. Mutum na zaune a Zangon Kataf jihar Kaduna zai rubuta ya na Gwadabawa a jihar Sokoto. Wani na Mangu a jihar Filato sai ya rubuta ya na Babura a jihar Jigawa ko Batagarawa a jihar Katsina. Mutum na zaune a Sabon Tasha jihar Kaduna zai rubuta ya na zaune a Shinkafi da ke jihar Zamfara. Suna kuma duk wanda ka ga ya rubuta shi ALHAWSAWI ne ko Bahaushe waye-waye to tantirin makiyin Hausawa ne don zai iya zama Emos Kaza, Damuna A na ruwa da sauransu. Wallahi duk ranar da mutanen nan su ka yi zuciya su ka fito da kan su, magana ta kare ko kadangare na Bokkos a Filato ba zai saye su sisin kobo ba.

Zayyane-zayyane kuma daga wata mata ta na tikar rawa wasu ‘yan iskan gari su na yi ma ta kida, sai mace tsirara, sai wani na busa k**ar baubawan burmi, sai wani ya daga hannu duk ya fusata k**ar kafuri ya ji kiran sallah. Kai hoton Hausawa a zuciyar mutanen nan ta yi muni.

Hakika yanda miyagun nan ke daukar al’adar Bahaushe cewa shagali ce ta rawa da waka da sharholia zai tabbatar ma na wadannan mutane ba Hausawa ba ne, hasalima yaki su ke yi da Hausawa da rigar karya ta Hausawa don kona kasar Hausa ala bashi su kafa kasar su ta MIDDLE BELT can kuma BIYAFARA su yi dabdala a Enugu. Rasar kunyar mutanen nan ta kai furta wai ba laifin da IPOB su ka yi wa Hausawa ko Arewa. Wani mugun yaro a cikinsu ma cewa ya yi bai san kisan gilla da mutan Gwanin Gora su ka yi ta yi ba, bai san kisan kare dangi da a ka yi wa musulmi a Zangon Kataf ba. Yanka matafiya a jihar Filato ma duk a wajensa shaci-fadi ne. Wani ma da ya yi mankas da kunu sai ya ce ‘yan Arewa munafukai ne sun ki magana kan ‘yan bindiga sun koma magana kan maharba da a ka kashe a jihar Edo! Shi a wajensa kar a yi magana kan kashe-kashe na Filato, kudancin Kaduna da Edo a koma batun ‘yan bindiga kadai na Arewa maso yamma. A fili ya nuna duk inda a ke kisan nan, garuruwan ‘yan Hausa zalla ne da yankinsu na kirkira wato MIDDLE BELT. Mun haska wani dan Eggon wato Alago da ke jihar Nasarawa da a ka dauka aikin Hausa zalla.

Ta hanyoyin daban-daban mun haska mutanen nan ba Hausawa ba ne kuma makiya kalmar shahada ne kazalika masoya IPOB ne. Zan haska wasu da har wa’azi su ke yi da sunan musulunci, amma shuka su a ka yi don su kunna wutar fitinar yaki tsakanin musulmi a Arewa.

A karshe k**ar yanda mu ka yi watsi da makiya Arewa da Najeriya su Ouba Ali Mohaman na K**aru, Kayode Salman Banjo da ‘yan IPOB da ke fesa fetur kan ciyayin kan jinkar Arewa; mu na godiya ga Allah da ya hutar da mu don miyagun nan da kan su, su ke tonawa kan su asiri, kuma dubunsu na gab da cika yayin da jami’an tsaro ke bincike kan su. Duk wani ALHAWASAWI da a ka cafke a maboyarsa kar ya ce ba mu gargade shi ba.

Nasiru Adamu El-hikaya

DAGA SALON RUBUTUN ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLAH KADAI ZA KA GANE ZAGON KASA SU KE YI DA RIGAR HAUSAWA, KUMA HARIN SU KAN MUS...
14/12/2025

DAGA SALON RUBUTUN ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLAH KADAI ZA KA GANE ZAGON KASA SU KE YI DA RIGAR HAUSAWA, KUMA HARIN SU KAN MUSULUNCI NE

HATTA ZAYYANE-ZAYYANE DA ZANE-ZANE DA SU KE YI, NA FITO DA HAUSAWA A MATSAYIN MA’ABOTA KIDA DA WAKA NE BA KARATUN TSANGAYA BA

Zagin Shehu Mujaddadi na kan gaba cikin alamun muguwar kwangilar makirci ta ‘yan karyar Hausa zalla. Hikimar zagin Shehu ita ce rushe jigo a tarihin hidima ga musulunci a wannan yankin na mu. Ko sau daya ba za ka ga miyagun nan na maganar mai ya sa Bature ya kawo addininin kirista har wasu daga masu bautar GIJI su ka shiga addinin su ka nemi yi wa GIJI da gizagizai kishiya ba. Ba za ka taba ji ko gani sun soki lamirin Turawa da su ka rika jidar karfafan mutanen Afurka ta yamma zuwa aikin gonakin reke a Amurka daure da sarka a matsayin bayi ba. Ba sa korafi kan kwashe dukiya da kayan tarihinmu da Turawa su ka yi.

Abu na biyu duk da ya gaza samun nasara tun daure Nnamdi Kanu shi ne jinjinawa Chukwua Nzegwu wanda ya sa bindiga ya harbe Firminiya Sir Ahmadu Bello da matarsa. Mai yabawa wanda ya kashe Sardauna a matsayin jarumi tabbas makiyin al’ummar Arewacin Arewa ne kuma makiyin musulmi ne. Ba a je ko ina ba sai mutanen su ka fito da ajandarsu ta mara baya ga wasu tsirarun ‘yan siyasa mabiya addinin kirista na Arewa ta tsakiya da su ka kirkiro sunan MIDDLE BELT. Na sa mu ku inda su ke cewa su na mara baya, MIDDLE BELT su fice daga Arewa. Asalin dalilin MIDDLE BELT shi ne kin jinin hatta alakanta yankin da Arewa don su a ganinsu sunan Arewa na Hausawa ne kuma ma’anarsa ta biyu musulmi!. Ban da Maguzawa da ke rakube a Arewacin Arewa, gaggan ‘yan karyar Hausa zalla ‘yan kananan kabilun wannan yankin ne da makiya Arewa su ka kirkira.

Mun sha haska Hausawan bogi da su ka fito daga Arewa ta tsakiya da su ne kan gaba wajen mara baya ga Bishop Wilfred daga Binuwai, wanda ya kai kara don neman Amurka ta kawo hare-hare Najeriya da nuna a na yi wa mabiya addinin kirista kisan kare dangi. Yau da gaskiya ta yi halinta har wakilan Amurka su ka shigo Najeriya sai tsit ka ke ji har sunan Wilfred na neman zama tarihi. Duk masu dogon baki da ke fatar ganin Amurka ta auna masallatan Jumma’a ta kawo hare-hare ko rutsawa da wasu ‘yan kauyukanmu su na wani taro k**ar hatsarin da ya faru kan masu Maulidi a Tudun Biri; sun ji kunya kuma sun shiga bakin ciki don mugun nufinsu ya ci tura. Ai kun ga ba su fadawa Amurka kisan da su ka yi a Gwanin Gora da Zangon Kataf ba.

Ga uku daga cikin manyan muradun ‘yan karyar Hausa zalla:

1.Tada fitinar yakin kabilanci tsakanin musulmi a kokuwar Arewa don karfafa makircin MIDDLE BELT da tallafawa IPOB da ‘yan ta’addansu ESN su ayyana kafa Biyafara.

2.Shiga rigar Hausawa don zuga Bahaushe ya dauka akwai wani musulunci daban da na Shehu Mujaddadi don haka ba lallai ya damu da zuwa masallaci ya yi sallah ba don wai limaman mabiya Mujaddadi ne. Nuna Kabila ta fi addini na daga hanyoyin yaki da riko da musulunci na Hausawa.

3.Rage karfin fada ajin Arewa a siyasance don ya zama za a iya yi wa manyan ‘yan siyasar Lardin sharri da cewa ‘yan kabila kaza ne don haka kar a zabe su. Hakan tabbas zai iya dora makiya karfin Arewa a kan madafu da za su iya wargaza Najeriya gaba daya ta hanyar ware musulmi daban sauran mutane daban. Akwai wani dan karyar Hausa zalla da ya taba alwashin za a iya neman musulunci a rasa a Arewa.

Da yardar Allah miyagu da iyayen gidansu, irin su Ouba na K**aru mai cillo harshen wuta Najeriya ya na yayyafa ruwa a K**aru ba za su ci nasara ba. Tuni ma muguwar manufarsu ta fara narkewa k**ar kankarar ruwan sanyi a rana.

Nasiru Adamu El-hikaya

LABARI MAI GIRGIZA KASA!Wannan shi ne *Hoton Musabaha ta Ƙarshe (Last Handshake)* a tsakanin manyan shugabannin biyu, wa...
04/12/2025

LABARI MAI GIRGIZA KASA!

Wannan shi ne *Hoton Musabaha ta Ƙarshe (Last Handshake)* a tsakanin manyan shugabannin biyu, wanda aka ɗauka wata huɗu (4) kacal kafin Yaƙin Bïafran ya ɓarke, ya shiga tarihi!

1. Yakubu Gowon: Shine Shugaban Ƙasa na Tarayyar Najeriya a lokacin.

2. Emeka Odumegwu-Ojukwu: Kuma Shine Wanda ya zama Shugaban Jihar Bïafra mai neman cin gashin kai.

Wannan Musabaha ce ta ƙarshe kafin dangantaka ta lalace kuma ƙasar ta shiga cikin mummunan yaƙi!

Tafiyar Ojukwu da Mĩƙa Waya

Odumegwu-Ojukwu ya kasance jagoran Bïafra tsawon lokacin yaƙin, daga Shekarar 1967 har zuwa 1970. Amma lokacin da aka cika shi da ruwa a gaba, ya yi abin da ya girgiza tarihi:

* Ya hau Jirgin Sama ya tsere zuwa ketare
* Ya bar Philip Effiong, wanda shine ke biye da shi a matsayi, don ya miƙa wuya ga Gwamnatin Tarayyar Najeriya a madadin Bïafra.

Wannan hoto yana ɗauke da ƙarin ma'ana fiye da yadda ake zato. Ya nuna wani lokaci na ƙarshe da aka yi fatan za a sasanta kafin faɗa ya fara.

Wane darasi kuka koya daga wannan gagarumin babi na tarihinmu?

Ku faɗi ra'ayoyinku a ƙasa! 👇

Gordon, wani tsohon bawa, ya na nuna tabo a bayansa sak**akon bulala da aka yi masa a Baton Rouge cikin jihar Louisiana ...
22/11/2025

Gordon, wani tsohon bawa, ya na nuna tabo a bayansa sak**akon bulala da aka yi masa a Baton Rouge cikin jihar Louisiana ta kasar Amurka

Ya tsere daga wata gona a Mississippi. Bayan da jami'an kiwon lafiya s**a ga tabon sai s**a bukaci a dauki hotonsa don rubuta shi a cikin tarihi. An yi masa bulala sau da yawa har tabo ya fara tasowa a kan tabo, an dauki hoton a shekarar 1863 Yau Shekaru (162) Kenan.

ABIN MAMAKI: Yadda Aka K**a Fasto da Zargin Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai a Jihar Filato.Najeriya ta shiga wani sabon babi...
16/11/2025

ABIN MAMAKI: Yadda Aka K**a Fasto da Zargin Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai a Jihar Filato.

Najeriya ta shiga wani sabon babi mai ban al’ajabi — Inda aka k**a wani malamin addinin kirista (Reverend Father) da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga muggan mak**ai a Jihar Filato da kewaye.

Eh, ka karanta daidai.
Wani limamin coci — wanda aka yarda da shi a matsayin mai addu’a, zaman lafiya da kare rayuka — yanzu ana zarginsa da taimakawa waɗanda ke hallaka al’umma marasa laifi.

Rahotanni sun ce jami’an tsaro sun gano yana *tsara safarar mak**ai iri-iri*, wanda ake zargi da taimakawa 'yan ta'adda wajen sace mutane, kai hari da kashe-kashe.

Yanzu sai na sake tambaya...

Lokacin da wasu daga cikinmu s**a ce *matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini bace*, mutane s**a ci mutunci, suna cewa muna goyon bayan mugunta.

Amma yanzu, me za su ce?

Shin waɗanda s**a yi gaggawar garzayawa Amurka suna kiran abun “kisan kiyashi ga Kiristoci” za su kai wannan labari wajen Donald Trump domin daidaita labarin?

Domin gaskiya ita ce:

Tsaro a Najeriya ba ya da addini.
(1) Ba ya sanye da zobon saliba ko tesbihu.
(2) Ba ya rike Alƙur’ani ko Littafi Mai Tsarki.
(3) Yana buya a daji, yana sayen mak**ai, yana halaka rayuka — Musulmi, Kirista, kowa.

Amma duk lokacin da aka fadi gaskiya, mutane kan mayar da martani da ji ba da hankali ba.

Wannan k**a ta bayyana gaskiya mai zurfi:

(1) Matsala laifi ce, ba addini ba.
(2) Mugaye suna ko’ina — a coci, a masallaci.
(3) Kuma yaƙi yana da su ne, ba da addininsu gabaɗaya ba.

Idan har Reverend Father za a k**a da kai wa 'yan bindiga mak**ai, to watakila... matsalar Najeriya ta fi “kisan kiyashi a ɓangare guda” girma da rikitarwa.

Mu kira gara gari.
Mu gyara matsalar tsaro — ba mu juya ta ta zama siyasa ko neman tausayi daga ƙasashen waje ba.

Daga: Abdul Mdk

CIGABAN MANTA SALLAH — MAI RUBUTU A TSAYEBayan da aka zauna gaban kwamiti domin binciken zargin da Mista Barry Burgess y...
10/11/2025

CIGABAN MANTA SALLAH — MAI RUBUTU A TSAYE

Bayan da aka zauna gaban kwamiti domin binciken zargin da Mista Barry Burgess yake yi a kan Getso, sai shi Barry ya ce yana son shirin Manta Sallah na mako na 5, 7, 10, da kuma ragowar ukun ƙarshe a fassarasu zuwa Turanci.

Hakan kuwa aka yi, domin ma, mai gaba ɗaya aka yi. Duka guda goma sha uku sai da aka fassarasu zuwa Turanci. Daga nan ne aka ba Halilu Getso damar kare kansa a kan zargin Barry.

Ya ce, da farko dai, wannan shiri ya ta’allaka ne a kan yadda rayuwar Turawa take, wato abubuwan da suke yi na al’adunsu da tsare-tsarensu waɗanda ba a sani ba. Sai kuma abubuwan da ba sa yi amma ake jita-jita cewa suna yi, da kuma waɗanda suna yi ɗin amma an juya labarin sama ta koma ƙasa.

Ya ƙara da cewa, misali: mu a Najeriya, akwai Hausawa da suke tunanin cewa Bature zai fito waje ya je majalisa ko wata maciya a ƙarƙashin bishiya ko rumfa ya zauna, a kawo masa abinci yaci, ko kuma ya fita wajen mai shayi a haɗa masa shayi da biredi da ƙwai 🥚 k**ar yadda tamu al’adar take.

To a can, sam, ba haka bane. Ya ce, mu bamu da juriyar bibiyar abu, ko da kuwa haƙƙinmu ne, bama iya kai-kawo wajen ganin an biya ko an bayar. Amma a can, idan akwai wani haƙƙi na mutum ko na gwamnati, to dole sai an bibiya.

Ya ce, maganar ta’addanci da Mista Barry yake cewa na ce Turawa suna yi, to bai fahimta bane. Wato farkon zuwana nan (London), na kunna talabijin a gidan da nake, sai naga wata mata da aka nuna cewa Allah ya bata haihuwa, kuma mace mai lalura ce. Ita kuma bata son ƴa mace, ballantana mai lalura.

Kullum sai ta fito da ita waje ta ajiye a kan keken masu lalura, ta barta a nan babu kayan kirki a jikinta, ga kuma dusar ƙanƙara 🌨️. Ita a dabararta, bata so a tuhume ta da laifin kisan kai, shiyasa take yi mata wannan azabar domin ta mutu ta huta.

To kuma da yake Allah shi ne mai kashewa da rayawa, sai gashi ta ƙi mutuwa, amma tana matuƙar shan wahala. Ko ni daga inda gidana yake a London zuwa ofishinmu na BBC, train 🚉 nake hawa. Kuma daga inda yake ajiyeni zuwa harabar BBC, yawanci rigata da hulata suna cike da ƙanƙarar snow.

Wannan labarin ba ƙirƙira bane, a labarai na gani kuma ana hira da ita wannan matar. Ku bincika, zaku tabbatar da cewa haka abin yake. A Afrika kuwa, abin mamaki ne a ce uwa ta yiwa ɗiyarta haka.
Sai na tambayi Mista Barry,

“Yanzu ka gamsu da abin da nake faɗa, ko har yanzu kana kan batunka na cewa ina ɓata muku suna?”

🧾 Batun bin haƙƙi

Getso ya ce, akwai abokin aikina da ya hau jirgin ƙasa daga wata unguwa a London zuwa wata unguwa, sai aka samu matsala, wato a inda zai sauka jirgin bai tsaya ba sai a tasha ta gaba.
Mai karɓar tikiti (ticket collector) ya rubuta masa adireshin inda zai biya ragowar kuɗin da ake binshi, sannan ya bashi da nashi adireshin.

Amma abokin aikin ya ƙi zuwa ya biya. Bayan wa’adin da s**a bashi ya cika, sai s**a sake rubuta masa wasika ta tunatarwa cewa har yanzu bai biya ba. Wani abin mamaki, wasikar haɗe take da kan sarki (official letter), kuma kuɗin kan sarkin sun fi waɗanda ake binshi yawa.

Sai dai duk da haka, s**a rubuta masa sau uku ba tare da gajiyawa ba, har sai da ya gaji da kanshi, yana mita da surutu, ya je ya biya haƙƙinsu sannan ya huta.

“Wannan abin cigaba ne,” in ji Getso.
“Zai nuna wa shugabannin Afrika da ‘yan Afrika yadda ake riƙe aiki da gaskiya da rikon amana.
Kuma zai haskawa al’ummarmu yadda ake bautawa ƙasa da gudummawar da kowane ɗan ƙasa zai iya bayarwa domin cigaban ƙasarsa.”

A taƙaice dai, kwamiti ya gano cewa Getso yana kan daidai, kuma ya bayar da umarni cewa ya ci gaba daga inda ya tsaya — saboda abin birgewa ne.

Saboda haka, bashi da wata matsala. An ba da damar ci gaba da shirin daga inda aka tsaya.

Wannan shi ne cikakken abin da ya faru tsakanin Bature Mista Barry Burgess da kuma Bahaushe Halilu Ahmad Getso a Rediyo BBC Hausa London.

© Jiya Ba Yau Ba.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.:

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram