Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.

Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. AN BUDE WANNAN SHAFI NE,SABODA TUNATAR DA KAWUKAN MU
BISA KYAWAWAN AL'ADUMMU NA HAUSA,

WADAN DA AYA Mungode

Dan Bunkasa Harshen Hausa da Al'adunsa,
Muna Maraba da shawarwarinku Domin wannan shafi naku ne.

KARIN MAGANA GUDA DARI 1.A daga sama! An yi wa wada kwace.2.A dauki kare ran farauta?3.A dauri kashi ko a bata igiya?4.A...
11/02/2026

KARIN MAGANA GUDA DARI
1.
A daga sama! An yi wa wada kwace.
2.
A dauki kare ran farauta?
3.
A dauri kashi ko a bata igiya?
4.
A aiki kare ya aiki wutsiya?
5.
A amshi kadai ne, ba a ga mutuwa ba.
6.
A bakin tsoho ne, goro kan tsufa.
7.
A bakin wawa, akan ji magana.
8.
A bar dariyar mai noma, ko bai sayar ba, ya ci abinsa.
9.
A bar ganin allura kankanuwa,karfe ce.
10.
A bar kaza, cikin gashinta.
11.
A bari ya huce, shi kan kawo rabon wani.
12.
A ci a sha, a rage don gobe.
13.
A ci ba a sayar ba, kwai ya fi doki.
14.
A ci yau a ci gobe, shi ne ci.
15.
A cikin ido, ake tsawurya.
16.
A haifi da da samu, ya fi a mutu a bar masa gado.
17.
A ja mu a kai! An ba uwar makaho kashi.
18.
A kashe wuta, tun tana kankanuwa.
19.
A lallaba a kai ta, in ta fito muna so.
20.
A lokacin da mage na nan, bera ba ya wasa.
21.
A mari matacce, don mai rai ya ji tsoro.
22.
A nema a samu, arziki ne.
23.
A nuna wa na rigingine farin wata?
24.
A raba arne da makami.
25.
A rabe da alwalar kifi a ruwa?
26.
A rabe magirbin yakuwa, da na rama?
27.
A rabu a gana, arziki ne.
28.
A rama wa kura aniyarta.
29.
A rashin kira, karen bebe ya bata.
30.
A rashin kula, akan kade kudi.
31.
A rashin sani, bako ya sha ruwan wanka.
32.
A rika sara, ana duban bakin gatari.
33.
A sa a baka, ya fi a rataya.
34.
A san mutum, a san cinikinsa.
35.
A sayar a fadi, karin wayo.
36.
A shekara saran ruwa, sai tambatse.
37.
A so kare, har jelarsa.
38.
A so uwa, a so 'ya'yanta.
39.
A tauna tsakuwa, don aya ta ji tsoro.
40.
A taya Allah kiwo, ya fi Allah na nan.
41.
A yi a gama, ya fi gobe a karasa.
42.
A yi abin da za a yi! Mahaukaci ya dauki rigar kurma.
43.
A yi maza, a fidda jaki daga duma.
44.
A yi wadda za a yi! Bera ya zubda garin kyanwa.
45.
A zaba a gasa, ta hana yaro suna.
46.
A zuba wa ungulu kwan zabuwa?
47.
Abin kwarai ya saba bacewa an dangana, ba takalmi ba.
48.
Abin al'ajabi! Ango ya kwanada kunzugu.
49.
Abin aljihu, na mai riga ne.
50.
Abin Allah! Budurwa da ciki; gwauro da yaye.
51.
Abin Allah! Budurwa da jika.
52.
Abin Allah, na Annabi ne.
53.
Abin aro, ba ya ado.
54.
Abin aro, bai rufe katara.
55.
Abin ba zai yiyu ba, auren mage da bera.
56.
Abin ba'a ne? An ce da kare mai sunan maza.
57.
Abin banza, hanci ba kafa.
58.
Abin biki, na biki ne.
59.
Abin cikin kwai, ya fi kwai dadi.
60.
Abin da aka gasa, shi ya ga wuta.
61.
Abin da aka shuka, shi yake tsira.
62.
Abin da Allah ya yi, Annabi sai ceto.
63.
Abin da babba ya gani daga zaune, yaro ko ya hau rimi ba zai linkaye shi ba.
64.
Abin da baki ya daura, hannubai iya kwancewa.
65.
Abin da dama ta jure, hagun ba ta jure ba.
66.
Abin da k**ar wuya! Gurguwa da aure nesa.
67.
Abin da ke ga amarya, shi takan ba ango.
68.
Abin da ke gidan Sarki, akwai shi a kasuwa.68.
Abin da ke gidan Sarki, akwai shi a kasuwa.
69.
Abin da kunya, uwar 'ya ta cinye suruki ran aure.
70.
Abin da mutum ya shuka, shizai girba.
71.
Abin da ruwan zafi ya dafa, in aka hakura ruwan sanyi ma ya dafa.
72.
Abin da wancan ya ce shi na ce! Kirarin mai tsoro.
73.
Abin da ya ba ka tsoro, wataran shi zai ba ka tausayi.
74.
Abin da ya ci Doma, ba ya barin Awai.
75.
Abin da ya ci ungulu, ba ya barin shaho.
76.
Abin da ya dami mutum, da shi yake mafarki.
77.
Abin da ya kewaye gida, gidan zai shiga.
78.
Abin da ya kora bera wuta, ya fi wutar zafi.
79.
Abin da ya taba hanci, ido saiya yi ruwa.
80.
Abin da ya zo, shi ake yayi.
81.
Abin daga Allah yake! Matar takaba ta yi ciki.
82.
Abin dariya! Yara sun tsinci hakori.
83.
Abin duniya mene ne? Kaza ta jawo muzuru kwanan gida.
84.
Abin duniya mene ne? Sarkinfawa da kyautar kaho.
85.
Abin fada, na mai baki ne.
86.
Abin majinyaci, na mai magani ne.
87.
Abin mamaki! Ciyawa da cin doki.
88.
Abin mamaki! Kare da tallan tsire.
89.
Abin mamaki! Kurege da fada wa zomo dadin kanzo.
90.
Abin mutum, abin wasansa.
91.
Abin na yi ne! An biya wa zawara hajji.
92.
Abin nema ya samu! Matar falke ta haifi jaki.
93.
Abin sai ido! Bebiya ta auri makadi.
94.
Abin shanya, ba a hana rana.
95.
Abin su na 'yan dangi, bare ina ruwanka?
96.
Abin tsana! Amarya a kan kare.
97.
Abin tsoro! Kura a rumbu.
98.
Abin wani da wuya, ne

10/02/2026

بسم الله الرحمن الرحيم
﴿إِنَّ اللَّهَ وَمَلَيْكَتَهُ يُصَلُّونَ عَلَى النَّبِيِّ يَأَيُّهَا الَّذِينَ امَنُوا صَلُّوا عَلَيْهِ وَسَلِّمُوا تَسْلِيمًا )

(الأحزاب: (٥٦)

BA MAMAKI DON MASU TARE HANYA, SU WARE MUSULMI SU KASHE DA TARWATSA NAMANSU, IN SUN DINKA RIGAR HAUSAWA DON RUSA AREWABA...
10/02/2026

BA MAMAKI DON MASU TARE HANYA, SU WARE MUSULMI SU KASHE DA TARWATSA NAMANSU, IN SUN DINKA RIGAR HAUSAWA DON RUSA AREWA

BA SU IYA HAUSA GARGAR DA BAKI BA, SHI YA SA SU KA BUYA DA SUNAYEN KARYA SU NA KULLAWA MUSULUNCI SHARRI

Tun ba soshiyal midiya akwai wannan kulli a zuciyar abokan gaban Hausawa don alakar Hausawa da musulunci. Duk tarihin miyagun kashe-kashe a baya ai an san wadanda su ka aikata k**a daga zubar da jinin Zangon Kataf, Yelwan Shendam har ma rikicin da ke faruwa a cikin Jos kafin ma na Gonin Gora. Duk Hausawa da a ke kira JASAWA sun san su waye ke kai mu su farmaki da kona gidajensu. A Jos ne masu kisan za su yi taro su raba gadon dukiyar Jasawa wai in sun kashe su, za su ci bulus, wannan ya ce shi zai zauna a gidan Alhaji wane ko ya mallaki motar Malam wane. Kai duk wanda ba dan Jos ba, ba lallai ya san zurfin fitinar nan ba. Har gobe akwai inda Jasawa ba sa iya shiga hakanan su ma masu ikirarin ‘yan kasa akwai sassan da ba sa marmarin zuwa don gudun abun da su ka shuka jiya. Akwai shekarar da su ka kai farmakin kisan kare dangi kan dandazon musulmi a masallacin idi a Jos. Ina Jasawa kun san wannan labarin. Waye ya taba fitowa ya ce ba a kyauta ba. Yau irin miyagun nan ne a soshiyal midiya su ka dinka rigar Hausawa.

Me laifin matafiyi da ya zo wucewa ta garinku. Wallahi sun kashe mutane a kan hanyar nan da ragargaza namansu da bunne su don kawar da shaida. Wani lokacin nisan kwana daga Allah kan tserar da wasu matafiyan in sun zo wucewa don hakika akwai matasa ‘yan gayawa-jini na wuce da ke marmarin su kashe. Kawai ka tare mutumin da ba ka sani ba ka kashe shi don addininku ba daya ba ne. Ba ma kisan kadai ba, wulakanta gawar. Akwai fa wani ma da matasan nan su ka make shi ya fadi sai wani mugu ya suntumo wani katon dutse ya ribza ma sa a tsakar ka! Wasu ma kan dau duwatsu su yi ta dandatsa naman gawawwakin matafiyan da su ka kashe. Shin akwai wani babba a masu kisan da ya taba magana da nuna hakan ba daidai ba ne? to hakika wadannan na kan gaba a ‘yan Hausa zalla da su ka hau soshiyal midiya su na ruruta fitinar kabilanci da zuga mutane su dau makami.

Gaba daya harkar Hausa zalla fa tunanin wasu mugayen mutane ne da su ka lura harshen Hausa na da tasiri kuma da shi malamai musulmi ke wa’azi wajen hada kan musulmi, su zama masu kaunar Allah da manzonsa. Damar boye suna a soshiyal midiya don ruruta wannan fitina ta zama mai sauki ga miyagun nan. Wallahi in Hausawa ne ba wanda zai boye sunansa ko amfani da hoton yaudara don bayyana ra’ayi. ‘Yan kalilan da ke fitowa ma a karkshin kasa su ke kunna wutar kuma sun ga za su iya zagin Shehu Mujaddadi su kwana lafiya. Nan gaba tabbas mutanen nan za su daina fakewa da zagin Fulani wajen sukar musulunci zuwa kan sahabbai ko ma su isa kan Manzon Allah mai tsira da aminci. Tunaninsu tun da su na boye ai ba mai iya gano su b***e ya dau mataki a kan cin mutuncin masu mutunci da su ke yi. Duk mai zabar kabila ta fi addini to kun san addinin da ya ke bi. Dama su addini ba wani abu ba ne a wajensu amma kiyayyar musulunci ita ce dabi’arsu, da ita a ka gina su kuma da alamu a kan wannan kiyayya za su mutu.

In wanda ba musulmi ba ya zunduma ma ka ashar ai ba mamaki don dama haka ya ke ji a ransa ya kashe ka ma ba komai. Fakewa da ‘yan ta’addan daji wai su na kashe su, karya su ke yi ko kazarsu ba a taba kashewa ba. Hasalima iyayen gidansu zuriyar IPOB ke samar da dabarun satar mutane ga barayin daji da kuma yi mu su safarar mak**ai da miyagun kwayoyi. Duk wani dan iska da ya ce ba su Chinedu ba ne ke kashe mutane a Arewa to shi ne Chinedun kura da fatar akuya. Kullum sai kara bude shafukan karya da sunan Hausawa su ke yi. Su fito fili in ba tsoro ba. Duk wanda ya boye kansa ya shigo nan ya na maganar banza to mun san ko waye kuma dubunsa zai cika zai kuma yabawa aya zaki. Ba gagararre sai bararre.

Nasiru Adamu El-hikaya

JIYA BA YAU BA: Tsohon Shugaban Kasa, Janar Babangida Da Matarsa, Marigayiya Maryam Babangida Da 'Ya'yansu
07/02/2026

JIYA BA YAU BA: Tsohon Shugaban Kasa, Janar Babangida Da Matarsa, Marigayiya Maryam Babangida Da 'Ya'yansu

TA YAYA ZA A YI MAKIYA SIR AHMADU BELLO ZA SU RIKA AMFANI DA TAMBARINSA A ALAMAR KUNGIYARSU TA IKIRARIN HAUSA ZALLAWalla...
07/02/2026

TA YAYA ZA A YI MAKIYA SIR AHMADU BELLO ZA SU RIKA AMFANI DA TAMBARINSA A ALAMAR KUNGIYARSU TA IKIRARIN HAUSA ZALLA

Wallahi duk mai zagin Sir Ahmadu Bello a nan dai Arewa azzalumi ne kuma mai goyon bayan masu zubar da jini ne irin ‘yan ta’addan daji, Chukwuma Nzeogwu da masu kashe matafiya haka siddan don kiyayyar bambancin addini. Tsayin daka da Gamji ya yi don ‘yan Arewa su samu ilimi su mulki Lardinsu NORTHERNIZATION POLICY ya jawo ma sa biyan sadaukarwar da ransa. Maimakon addu’ar rahama sai makiya su ka murde tarihi su ka dinka rigar karya ta Hausawa don haddasa yakin kabilanci a Arewa. Ina gidajen Sardauna? Ina muk**an da ‘ya’ya ko jikokinsu Sardauna ke rike da su? babu wani abu na son zuciya da wani zai nuna amma mu za mu nuna jami’ar ABU a Zaria, za mu haura da mutum Tsaunin Mambilla, za mu zagaya da mutum cibiyoyin ilimi da tsoffin kolejojin horar da malamai da duk su ka samu albarkacin Gamji. Ga ayyukan alheri barjak.

Yayin da ‘yan ikirarin karya na Hausa zalla ke cewa sam ba Arewa sai dai HAUSALAND don haddasa fitina, a lokaci guda sun dauki daya daga alamun da su Gamji da abokan aikinsa su ka tsara don hadin kan al’ummar Arewa wato DAGIN AREWA ko TAMBARIN AREWA sun makala a mtsayin alamarsu! Tubka da warwara kenan. Mutanen nan shirme kawai su ke yi da biyewa ‘yan IPOB don kai Arewa kasa. Ba Hausawa ba ne kuma ba su da alaka da Hausawa sai in annamimanci ya ratso.

SHAWARA

Mutanen kungiyar nan da ke murde tarihi da gangan, ko dai su canja wannan tambari zuwa na MIDDLE BELT ko BIYAFARA ko kuma su tuba daga wannan mugun aikin. Hakika sun bi hanyar da har abada ba za ta bulle ba.

Nasiru Adamu El-hikaya

Allah ka jikan Sheikh Rigi-Rigi.yasa Aljanna Makoma.
02/02/2026

Allah ka jikan Sheikh Rigi-Rigi.yasa Aljanna Makoma.

BA TANTAMA ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA MUSULUNCI NE BA SA SO, DON SUN YI WATSI DA SUNAYEN MUSULMI WAI A KOMA NA GARGAJIYAMIY...
01/02/2026

BA TANTAMA ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA MUSULUNCI NE BA SA SO, DON SUN YI WATSI DA SUNAYEN MUSULMI WAI A KOMA NA GARGAJIYA

MIYAGUN NA FAKEWA DA ZAGIN SHEHU MUJADDADI NE DON KUSHE MUSULUNCI DA NUNA KIYAYYA GA MANZON ALLAH MAI TSIRA DA AMINCI

Shafin THE NIGERIAN BAHAUSHE ya yi wuf ya wallafa wani rubutu da daya daga ‘yan Hausa zalla Aliyu Ammani ya rubuta tun 2019 ya na nuna fargaba cewa sunayen gargajiya na Hausawa za su bace don daukar na Larabawa. Ammani bai tsaya ba sai da ya caccaki wani abu da ya zayyana da wankewa Hausawa kwakwalwa da nau’in musulunci na daban da Jihadin Sokoto (na Shehu Mujaddadi) ya kawo na goge duk wasu alamu da al’adu na Hausawa kafin zuwan musulunci. Ammani dai a nan bai kawo aya ko Hadisi daga Alkur’ani ko BIBLE da ke nuna wani nau’in musulunci ko addini ne da ke da ka’idar adana alamu da al’adu na Hausawa kafin zuwan musulunci ko kiristanci ba. Shin idan musulmi su ka dauki sunayen Larabawa, kirista su ka dau na Turawa me bambancin a nan. Duk rubutun na sa bai soki Turawa da su ka shigo bayan Jihadin ba a 1903 da a ka yi ruwan sunaye irin su John, Jacob, Peter, Daniel Musa, Paul Audu da sauransu.

Ammani ya kara da cewa idan Bahaushe ya radawa dansa suna Faisal ko Fahad wato tsoffin sunayen sarakunan Saudiyya ba malami (musulmi) da zai yi magana. Sai ya ce amma in an juya sunayen kai tsaye zuwa Hausa wato TAKOBI ko DAMISA za a yi mamakin irin kururuwar da za a yi. Mutumin nan bai tsaya nan ba sai da ya dira kan kabilancinsa da nuna Fulani na radawa ‘ya’yansu Bello, Tukur, Sambo kuma ba wanda ya ke duba sahihancinsu a musulunci. A nan ya nuna ai duk sunayen Muhammadai ne wato misali Muhammadu Bello ko Muhammad Tukur da wato ba malamin da ke korafi, sai caraf ya kara dira kan manufarsa ya na mai cewa amma in an ambata Muhammadu Jan-Gwarzo, Muhammadu Jan Hazo, Muhammadu Korau da sauransu sai a dauka ko soke su da sabawa musulunci. Tambaya a nan shin waye ya dauki wadannan sunaye sun sabawa musulunci? A ina? A ABU, BUK, UDUS ko FUDMA ta su Daniel Danladi Musa?.

Nan masu muhawara su ka shiga nuna ai su in sun haifi ‘ya’ya sunayen Hausawa za su saka wato don su ba wa Shehu Mujaddadi haushi. Shin Mujaddadi Balarabe ne ko shi ne addinin musulunci? Shin tun kafin Jihadin Shehu ba a yi Sarkin Kano Muhammadu Rumfa ba? Ba a yi mai sunan Larabawa Muhammadu Al-Walid ba? Su ma Jihadin ne ya kakaba mu su sunayen ko akwai makiya musulunci a tsakanin wancan zamani gabanin Jihadi da su ka bunne musulunci su ka dauki tsafe-tsafe da camfe-camfe da rawar banjo?.

Shi kansa marubucin Aliyu Ammani tun 2019 zuwa yau bai sauya sunansa ALIYU na Larabawa ba. Shin ko Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar ne ya tilasta shi ya cigaba da amfani da sunan? Mutanen nan su na yin abun da su ka ga dama kuma akwai manufar da su ke boyewa. Akwai wani matashi ma mai sunan Sahabban Manzon Allah Abubakar da Usman (Aboubakar Cerdic Ousmane) da ya nuna mahaifinsa ba zai hana shi sauya sunansa ba in ya na so, kuma shi in ya haifi yara sunayen gargajiya na Hausawa zai saka da ke nuna ya na matukar tsanar sunayen sahabban Manzon Allah. Da ya ke mutanen ma kirkirar sunayen su ka yi ba sunan gaskiya, ba hoto ba adireshi don haka ko yanzu za su iya kakalo wani sunan don batar da sawu. Wani abun takaici ma na rashin sanin ya k**ata, sai ma ‘yan ikirarin Hausa zalla na kirkirar sunayen musulunci da na Larabawa k**ar AL-HAWSAWI, AL-FARISI, ALKANAWY da sauransu, su na makalawa kansu. Hakika duk su na yin hakan ne don dabarun bagaye ko basaja don a dauke su masu bin musulunci sau da kafa don samun logar yaudarar al’ummarmu a bi kiran da su ke yi na aukawa gubar kabilanci.

Wallahi na samu sahihin labarin wasu daga masu ruruta fitinar nan jikokin jami’an soji ne da Turawa su ka yi amfani da su wajen rusa Daular musulunci ta Sokoto don haka sun gado kiyayyar ce.

Gari ya waye duk an gane wakilan su Chukwuma da Kanu, kuma ba za su yi nasara ba. Yo ba akwai ma wani a cikinsu da sunansa kakaf takwaran mahaifin Manzon Allah ba ne? su shiga sauya sunayensu ma na zuwa gargajiya ai tsarin mulkin Najeriya bai hana su radawa kansu sunaye har irin su Bob Marley ko Zidane Kajuru ba.

Nasiru Adamu El-hikaya

MAGUZAWA, MIDIBELAWA DA IPOB NE SU KA YI MAJA SAI SUN KAI AREWA KASASHIN IN BA A WAJEN MAGUZAWA BA INA ZA KA JI MAI ALAK...
01/02/2026

MAGUZAWA, MIDIBELAWA DA IPOB NE SU KA YI MAJA SAI SUN KAI AREWA KASA

SHIN IN BA A WAJEN MAGUZAWA BA INA ZA KA JI MAI ALAKANTA HAUSAWA DA BAUTAR GIJI?

Hatta wanda ya karanta hamshakin littafin MAGANA JARI CE na Dokta Abubakar Imam da kulawar Bature RM East zai san tsakanin Hausawa da Maguzawa hanyar jirgi daban ta mota daban. Maguzawa wasu kabilu ne a Arewa ‘yan gargajiya da su ka narke a jikin Hausawa kuma su na bin addinin Maguzanci da ke da babban alla mai suna GIJI mai kananan alloli gizagizai sai taimakon aljana Doguwa da sauransu. Ba wanda ya hana su bautawa GIJI kuma ba mai tsangwamar kowa kan addinin da ya zaba a karkashin kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 (Gyararre)

Har ila yau mai shafin nan na NIGERIAN BAHAUSHE wanda mun fahimci kowaye kuma za mu haska shi da tarihinsa da muradunsa; ya sake wallafa rubutu da ya ke cewa “Ina masu kiran Hausawa Maguzawa? Madalla da Maguzawa” Kun ga a nan marubucin na kokarin makala kansa karfi da yaji ga Hausawa da kirkiro tambaya wai ina masu kiran Hausawa Maguzawa. Ko a zantawar da na yi kwanan nan da masanin harshen Hausa Farfesa Aliyu Muhammad Bunza ya tabbatar da akwai wasu kabilu hatta a Kano da su ka narke su ka zama Hausawa. Tabbas biri ya yi k**a da mutum don wadannan kabilun da su ka taho daga wasu sassan Afurka na rike da addininsu na gargajiya kuma ba za su iya shiga musulunci ba don zai haramta mu su tsafe-tsafe, rawar banjo da bautar GIJI. Irin wadannan kabilun masu shigar burtu na kan gaba a sojojin da Turawan mulkin mallaka su ka dauka wajen yaki da Daular Sokoto su ka kashe daruruwan mutane da fille kan su. Kaunar Bature ta sa wasu daga ciki sun karbi addinin kirista amma har gobe akwai wadannan kabilu masu aron harshen Hausa su na shigar burtu da bautar GIJI kuma su ne su ka samu soshiyal midiya a bagas don ruruta fitinar kabilanci da zummar wargaza Arewa ta musulmi don cimma dogon burin taya abokan burminsu IPOB su kafa Biyafara da Midibelawa su ware wai su sam ba Arewa ba ne tun da ai Arewa an fiye sallah da salati su kuma ba sa so.

Mayaudarin marubuncin nan ya ce Maguzawa sun gina masallatai tun fiye da shekaru 700! Wanda ya gina masallaci amma ba ya sallah? Wallahi karya ya ke yi ya na kare tafarkin iyayensa ne kawai da cin zarafin addinin musulunci. Wautar ita ce mutanen nan sun dauka in sun yaki musulunci to sun yaki Shehu Mujaddadi ne. Ko ka ji dan IPOB na cewa THE BRAND OF ISLAM SMUGGLED INTO ZOO wai wani nau’in musulunci da a ke amfani da shi a Arewa, ko in ya yi tatil da giya ya ce ai musulunci addinin Larabawa ne mu bar mu su kayansu mu koma gargajiya!. Wani dan Midibelawa don nesanta kan su da musulunci ya ce alamarsu cin naman alade da kare. Ga hoton a kasa.

Mai ya sa Maguzawa ba za su fito fili su kafa wajajen bautar su ba su daina basaja? In Bamaguje zai gina masallatai to mai ya sa ba zai gina wajen ibadarsa ta bautar GIJI ba? Ka ji soki-burutsu. Yo wadanda su ka gina masallatai fiye da shekaru 700 amma su na kamfen a soshiyal midiya na kabilanci da sunan Larabawa da hotunan karya ba adireshi? Zancen banza. In ba tsoro ba su fito fili ma na, iyye ‘yan butan-uwa. Kai kai ku rufawa kan ku asiri don wallahi in na tono wani abu ko aikin nan na barandar IPOB da ku ke yi za ku yi murabus.

Nasiru Adamu El-hikaya

ZIYARAR ‘YAN HAUSA ZALLA MASARAUTAR DAURA TA HASKA GIRMAN HAUSA YA WUCE KUNGIYAR HAUSA ZALLASARAUNIYA DAURAMA TA AURI YA...
01/02/2026

ZIYARAR ‘YAN HAUSA ZALLA MASARAUTAR DAURA TA HASKA GIRMAN HAUSA YA WUCE KUNGIYAR HAUSA ZALLA

SARAUNIYA DAURAMA TA AURI YARIMA BAYAJIDDA (ABU YAZID) BALARABE TA HAIFI BALARABE SARKI BAWO, MAHAIFIN 6 DAGA SARAKUNAN HAUSA 7

Tun bara na so yin kebantaccen sharhi kan ziyarar ‘yan Hausa zalla Daura amma ban samu dama ba, sai dai na rika buga misalai. A ziyarar dai wakilin mai martaba sarki kan tarihi ya yi bayani na abun da ya sani kan harshen Hausa da wani bincike ya nuna ya fito ne daga harsuna 3 da su ka hada da BERBER, ZULU da Mandingo. Hakan na nufin wasu kabilu kan hadu a wata magama a sanadiyyar hijira, fatauci, wa’azin addini ko gano girman duniya don haka ya zama lallai su samu wani harshe da zai zama na bai daya da za su rika amfani da shi, ko su rungumi harshen da ya fi saukin koya a tsakaninsu, sai su yi ta kwatance-kwatance har su fahimci juna su rike wannan harshen da shigo da sauran harsunansu a hankali cikin wannan mai saukin har ya ginu ya zama harshensu. Yo in ba haka ba yaya BERBER daga Afurka ta Arewa, Zulu daga Afurka ta kudu da Mandingo daga wajen Gambia, Mali da Senegal A nan Afurka ta yamma za su samar da Hausa? Binciken ya nuna harsunan su na dauke da kalmomin Hausa na asali gabanin shigowar Larabci a sanadiyyar addinin musulunci.

Yauwa idan mu ka bi ka’idar ‘yan Hausa zalla cewa in mahaifinka Bahaushe ne to ko mahaifiyarka Balarabiya ce ko Baturiya to kai din Bahaushe ne. In mun yi amfani da sahihancin tarihin Daular Daura za mu ga Abu Yazid Balarabe ne daga Bagadaza da ya auri Bahaushiya sarauniya Daurama ya haifi Balarabe mai suna BAWO, shi kuma Balarabe Bawo ya haifi 6 daga sarakunan masarautun Hausa 7; Kano, Katsina, Zazzau, Daura,Gobir, Rano da Hadejia da ta kafu daga dan Bayajidda Balarabe mai suna Biram da ya Haifa daga matarsa ‘yan sarkin Borno. Ka’idar ta ‘yan Hausa zalla ce da wasu ke fakewa da musulunci kan matsayin mahaifi a wajen ‘ya’ya. A musulunci ka’idar sam-sam ba ta karfafa kabilanci ko kabila ba, amma ta na umurtar kiran ‘ya’ya da sunayen mahaifansu maza. Mai bincike ya koma kan tarihin babban sahabi Zayd ibn Haritha.

Maimaicin sashe kan rubutuna na baya, na bayyana yadda masana tarihi da kuma harshen Hausa ciki da Farfesa Aliyu Muhammad Bunza na cewa akwai wasu kabilu hatta a Kano da su ka narke su ka zama Hausawa amma akwai asalin yarensu daban. Na ce biri ya yi k**a da mutum, a cikin su ne a ka iya samun Maguzawa da ke bin addinin gargajiya kuma har gobe su na nan jikin Hausawa duk da ba sa sha’awar addinin musulunci don zai hana su rawan gaban hantsi. In Allah ya yarda nan gaba za mu duba me bambancin Kanawa masu Kananci da Katsinawa masu Katsinanci da Gobirawa da za a fi ganewa su na Sakkwatanci. A taba-ka-lashe zaman gari na iya shafar salon karin harshe. Ku saurari Hausawa daga Ghana ku ji karin harshensu ya samu ne a dalilin cudanya da kabilun kasar Ghana. Hausawa a Sudan ko Saudiyya na da salo mai cike da Larabci ma kai tsaye. Shin me wagga magana ka nuhi, alkawalin Allah zwan hiddota swala-swala!.

Nasiru Adamu El-hikaya

01/02/2026

Assalamu Alaikum, ‘yan uwa ku kalli ziyara da ‘yan Hausa zalla su ka kai Daura kimanin shekaru 2 da su ka wuce kuma su ka ce mai martaba sarki ya ba da umurnin a ba su tarihin Hausa da Daura. A lokacin ba su gama fito da muradunsu na kabilanci ba, don tarihin harshen Hausa su ka nema ba na Hausawa ba. Kowa ya san harshen Hausa na daga manyan harsunan duniya da kauyanci ne wani kawai ya bugi kirji ya ce mallakarsa ne don mummunar manufa. Wakilin sarki ya bayyana wani bincike da a ka gudanar cewa harshen ya fito ne daga harsuna 3 da su ka hada da BERBER (BABA), Zulu daga Afurka ta kudu da Mandingo. Wakili ya ce harshen Larbaci ma ya na da yawa a Hausa. Ma’ana a nan duk babban harshe kan samo asali daga hadin guiwar harsuna daban-daban k**ar yadda turancin ingilishi ya samo asali daga kabilun ANGLES, SAXONS DA JUTES inda yaren LATIN DA NORMAN FRANCE su ka kutsa cikinsa👇👇👇👇

MAGUZAWA DA MIDIBELAWA KE BASAJA DA HAUSA ZALLA DON YAKI DA MUSULUNCISU KAN FAKE DA ZAGIN SHEHU MUJADDADI DON KUSHE DOKO...
01/02/2026

MAGUZAWA DA MIDIBELAWA KE BASAJA DA HAUSA ZALLA DON YAKI DA MUSULUNCI

SU KAN FAKE DA ZAGIN SHEHU MUJADDADI DON KUSHE DOKOKIN MUSULUNCI DA TALLATA KAFURCI

Duk wata karyar nuna takaici kan ta’addancin barayin daji da ‘yan karyar Hausa zalla ke yi ba gaskiya ba ne sam. Ba sa kaunar jin duk wata hanya ta karewar fitinar nan don ai ba ta shafe su ba, kuma hajar cigaba da kada gangar kwangilarsu ce. Tamkar yadda iyayen gidansu musamman IPOB su ka bude shafuka barkatai, su ma haka su ka yi amma ba su kai mizanin yawan na IPOB ba don sau da dama sai ma ‘yan IPOB din kai tsaye sun shigo sun kawo mu su dauki don kara ruruta fitinar kira ga wadanda su ke son yaudara su dau mak**ai su shiga kashe-kashe kuma ba maganar nufar daji ba, a’a kan shugabannin addinin musulunci k**a daga amfani da masallatan Jumma’a zuwa kasuwanni da tare hanya a yi kisa sai a fake da wai kare kai ne k**ar yadda ku ka ga sun yi a hukuncin Zidane Kajuru. Kwata-kwata a wajensu fiye da mutum 66 da Kajuru ya ja zuga su ka shekar da jininsu ba mutane ba ne.

Kazalika duk wanda ke nuna illar ruruta fitinar kabilanci, sai su yi caraf su zayyana shi da mai goyon bayan barayin daji. Wannene ba wannene ba, fitinar kabilanci ko barayin daji su waye ne za a kyale. Kakaf hukuma ta murkushe su a huta. Ai kun ga Nnamdi Kanu da ya zama waliyin ruruta fitinar kabilanci a Arewa da labarun tatsuniyoyin karya har da labarin Jibrin na Sudan, yau an wayi gari ya girbi shukar tsiyar da ya shuka har da riba.

Wani shafi mai ikirarin Hausawa ya yi irin wannan izgilanci day a samu sambarka daga ‘yan IPOB. Shafin ya wallafa labarin dan kwallon Senegal Sadio Mane wanda ya yi biris da wata tsigalalliya da ta nemi rungume shi a filin wasa da nuna shi musulmi ne. Shafin sai ya kawo Muhammad Salah na Masar wanda shi kuma ya amince wata tsigalalliya ta rungume shi wai ya burgeta kenan a kwallo. A nan shafin ya nuna matsalar ba addini ba ne kawai ra’ayi ko imanin mutum ne. Sai shafin ya cikata da ayar ‘yan iska wai LET LOVE LEAD wato a bar soyayya ta yi dabdala in an zo shakiyanci na kare fasikanci. Sam ba za mu amince da LOVE irin wannan na ‘yan banza ba. Na ga wani ma don ya gaji da jiran a fara yaki ya shiga tallata wata katuwar bindiga. Haka nan wani ma mai basajar bai san bambancin Allah SWT da Manzon Allah SAW ba da ya tashi zagin Shehu Mujaddadi. Lallai hukumomi su yi farautar miyagun nan na soshiyal midiya don gudun kar su ribaci wadanda labarinmu bai je mu su ba cewa mutanen nan ba sam ba Hausawa ba ne kuma makiya musulunci da Arewa ne.

Nasiru Adamu El-hikaya

KAWAI ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA SU MARAWA DAN TAKARARSU NA IPOB BAYA SU DAINA KAME-KAMEIPOB NA KARKATA ZUWA TRUMP YA MATSA...
21/01/2026

KAWAI ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA SU MARAWA DAN TAKARARSU NA IPOB BAYA SU DAINA KAME-KAME

IPOB NA KARKATA ZUWA TRUMP YA MATSA LAMBA A KAFA BIYAFARA KO A YI ZABEN RABA GARDAMA

SU WAYE KE SAFARAR MAKAMAI GA BARAYIN DAJI, SU WAYE SU KA KOYA MU SU SATAR MUTANE? SU WAYE KE SHIGO DA MIYAGUN KWAYOYI AREWA?

Farko dai duk mai nazari ya tabbatar ‘yan karyar Hausa zalla ba Hausawa ba ne ko kuma don a kara fahimta makiya Hausawa ne don sun fi karfafa a jingine addini a koma zamanin jahiliyya na kabilanci. Duk wannan don tsananin kiyayya ga musulunci ne. Miyagun sun yi ta neman yaki da musulunci ta hanyar jifar addinin da cewa FODIYANCI ne kuma duk musulmi, ya san ba wani abu mai k**a da wannan a nan Najeriya ta Arewa. Sun ce kar a bi limami Bafulatani sallah don neman a hargitse da fitina tsakanin musulmi amma hakan ya gagara! Wato shi wanda ba musulmi ba, don zuciyarsa ta rube da cin naman alade da kora giya a kai, ba ya iya tunani kan musulunci da ma’auni mai kyau sai kokarin gwada addinin ya ke yi da addinan ganin dama. Wannan makirci ya ki samun karbuwa duk da maimaita shi kullum da yaran nan masu zaman kashe wando, da a ka dauka su ka zama zuga-zugin kunna wannan wutar.

Matar nan mai yaki da Igbo musulmi da na saka mu ku bidiyonta, ta ce hatta maganar Igbo musulmi kokarin haddasa fitinar hana Peter Obi samun nasarar siyasar 2027 ne. Gaskiyar magana Obi ya so yin kuskure a 2023 da ya hau doron addinin kirista wajen kamfen don shugaba Tinubu ya tsayar da mataimaki Sanata Kashim Shettima Musulmi. Tun da IPOB ba ta da shugaban Biyafara fiye da Kanu, amma a tsarin siyasar tarayya ta na son marawa Peter Obi ne baya. Akalla ko Peter Obi bai zama shugaba ba kai tsaye ya zama mataimaki don haka ne hanyar share fagen samun shugabanci. Kuma ta hanyar shugaban kasa za a iya kiran zaben raba-gardama don kafa Biyafara. Mu mun yi imani Allah ne zai fito da shugaban Najeriya a 2027 ba tada jijiyar wuya ko farafagandar wani mugu a yanar gizo ba.

Igbo ‘yan IPOB da ke fita kasashen duniya baya ga duk garuruwan Arewa don neman kudi ta ko wace hanya, na tunanin dawo da Biyafara don samun kudi ne da yi wa sauran sassan kasa mugunta. Ai farko Biyafara ta hada har da jihohin kudu maso kudu masu man fetur. Biyafarar Ojukwu ta kabilanci ce amma wannan Biyafara ta neman kudi da mulki ne fiye da kabilancin. Rashin al’adu masu kyau da rashin shugabanci na bai daya irin wanda Mujaddadi ya kafa a yankin Arewa, ya sa ko Biyafara ta yiwu, to mutanen ba za su taba zama lafiya tsakaninsu ba don babban burinsu a duniya tara kudi, kuma ko addinin kirista da su ke yi ba ya hana su safarar miyagun kwayoyi da kashe-kashe don neman kudi.

IPOB ke ingiza kamfen din Hausa zalla da tsara hanyoyin da za a wargaza Arewa don rage karfin mulki a tarayya a samu kafa Biyafara a bulus. Duk mai yawo a soshiyal midiya zai ga kalmomin da ‘yan karyar Hausa zalla ke yayatawa wankowa su ke yi daga IPOB. Su waye ke safarar mak**ai ga barayin daji? Su waye ke shigo da miyagun kwayoyi Arewa? Su waye su ka horar da barayin daji dabarun satar mutane?.

Hausa-karya maimakon batawa mutane lokaci ku shiga kamfen ga dan takararku na IPOB mu ga abun da Allah zai yi a 2027 ku daina wahalar da kanku da annamimancin nan. In kun kona Arewa hatta yankin da ku ke kaunan MIDDLE BELT ba zai tsira ba. Ina amfanin badi ba rai.

Nasiru Adamu El-hikaya

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.:

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram