15/02/2026
Yana daga cikin alamun imani kauna saboda Allah da kiyayya saboda Allah duk Wanda Zaka soshi to ka tabbata Don Allah Zaka soshi hakama idan Zaka kishi to ka kishi saboda Allah
A yanzu danake magana bansan abinda gobe zata haifarba Amma Ina fatan alkhairi acikin zuciyata inason inga mutum Mai kishin addini Mai son kawo Gyara Mai fada da barna koda bansan inda yafitoba Kuma idan Dan siyasa ne zangoyi bayansa ako wace jam'iyya yake
Haka zalika inajin bacin rai ga Wanda yazama kishiyar haka koka gida daya muke jini daya, inason inyi amfani da wannan damar inyi Kira zuwaga yan uwana musamman matasa mu canza tunanimmu na neman biyan bukatummu kawai batareda Sanya manufar addinimmu gaba ba
Idan zakayi yabo ko zagi kafin kayi kafara tunani shin maslahar addini ce tasa Zan yabe wane ko in sokeshi kokodai bukatatace kawai yan uwa mu tuna cewa babu wani Abu da Zaka samu ko yasameka face an rubuta haka tun kafin kazo duniya
Annabi S.a.w Yana cewa
ان روح القدس نفث في روعي انه لن تموت نفس حتى تستكمل رزقها واجلها فاتقوا الله واجملوا في الطلب ولا يحملن احدكم استبطاء الرزق ان تطلبوه بمعصية الله فانما عند الله لا ينال بمعصيته
Ma'ana"Hakika Ruhi Mai tealki(Mala'ika jibrilu) ya saukarda wahayi zuwagareni cewa babu wata rayuwa dazata mutu har Sai ta kammala canye arzikinta da kuma ajalinta saboda haka kuji tsoron Allah kubi hanya Mai kyau wajen nema kada jinkirin zuwan arziki yasa kunemeshi ta hanyar sabon Allah domin abinda ke wajen Allah ba'a samunsa ta hanyar sabamasa"
Wannan tunatarwace daga Dan uwanku
Abdullahi Sambo Dandin-mahe
Allah yasa mugane.